Masu zaɓe a jihohi huɗu a ƙasar nan sun fara kaɗa ƙuri’a don zaɓen sabbin shugabannin ƙananan hukumomi da kansiloli.
Jihohin da ake gudanar da zaɓukan a yau sun haɗa da Rivers da Benue da Akwa Ibom da kuma jihar Jigawa.
Ana hasashen cewa jam’iyyu masu mulkin jihohin ne za su lashe duka zaɓukan ƙananan hukumomin da na kansiloli.
Ko a baya-bayan nan ma zaɓukan ƙananan hukumomi da aka gudanar a wasu jihohin ƙasar, jam’iyyu masu mulkin jihohin ne suka lashe duka kujerun.
Wannan wata al’ada ce ta zaɓukan ƙananna hukumomi a Najeriya, lamarin da masu sharhi ke ganin cewa na daga cikin abubuwan da ke rage wa zaɓukan ƙananan hukumomin karsashi da farin jini.
Haka kuma wasu na fargabar hakan ka iya kawo cikas ga hukuncin kotun ƙolin ƙasar, na bai wa ƙananan hukumomin cikakken ‘yancin cin gashin kai.