David Adeleke, wanda aka fi sani da Davido, ya caccaki gwamna Gboyega Oyetola na jihar Osun saboda kalubalantar nasarar kawunsa, Sanata Ademola Adeleke a kotun sauraron kararrakin zabe.
Ku tuna cewa a ranar Juma’a ne Gwamna Oyetola ya garzaya kotun sauraron kararrakin zaben gwamna da ke Osogbo domin kalubalantar nasarar Adeleke.
Gwamna Oyetola ya mika bukatar a ranar Juma’a tare da daya daga cikin lauyoyin masu kara, Kunle Adegoke (SAN) a babbar kotun jihar Osun, Oke-Fia, Osogbo, babban birnin jihar.
Da yake mayar da martani, Davido a shafinsa na Twitter ya ce rashin nasara yana da zafi kuma ya bukaci Oyetola ya taya Adeleke murna.