fidelitybank

Zaɓen Najeriya ya gaza cimma yadda ‘yan ƙasar suka yi tsammani – Amurka

Date:

Sama da mako guda bayan gudanar da zaɓen shugaban ƙasa a Najeriya, Amurka ta ce, zaɓen ya ya gaza cimma yadda ‘yan ƙasar suka yi tsammani.

Hukumar zaɓen ƙasar ta ayyana Bola Ahmed Tinubu na jam’iyyar APC a matsayin wadda ya lashe zaɓen da adadin ƙuri’u 8,794,726, tazarar ƙuri’a kusan miliyan biyu tsakaninsa da Atiku Abubakar na jam’iyyar PDP.

Atiku mai shekara 76, ya samu ƙuri’a 6,984,520, yayin da Peter Obi na LP – wanda a ƙasa da shekara guda ya tara matasan mabiya- ya bayar da mamaki a takarar inda ya samu ƙuri’a 6,101,533.

To sai dai Atiku da Obi dukkansu sun yi zargin maguɗi a zaɓen, inda suka sha alwashin ƙalubalantar nasarar Tinubu a kotu.

A wata sanarwa da Amurkan da fitar ta hannun jakadiyar ƙasar a Najeriya Mary Beth Leonard, ta ce ‘yan Najeriya da dama sun fusata game da sakamakon, inda wasu suka riƙa murna kan nasarar da suka samu.

Sanarwar ta ƙara da cewa “A bayyane take cewa tsarin zaɓen Najeriya da aka gudanarar ranar 25 ga watan Fabrairu ya gaza cimma yadda ‘yan ƙasar suka yi tsammani,”

“Kamar yadda na sha faɗa a baya gabanin zaɓen, Najeriya ta cimma abubuwa masu yawa a tsawon shekaru sama da 20 da ta yi bayan komawa tafarkin dimoraɗiyya, kuma ci gaban da aka samu a fannin zaɓukan ƙasar na daga cikin nasarorin da ƙasar ta cimma”

“Yan Najeriya sun nuna sadaukarwarsu ga dimokraɗiyya ranar 25 ga watan fabrairu, to sai dai da yawa sun nuna fusata, yayin da wasu da dama suka nuna murna bayan nasarar da suka samu”. In ji BBC.

nigerianewstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...
X whatsapp