Yayin da aka fara kaɗa ƙuri’a a rumfunan zaɓe da dama da ke Lokoja, babban birnin jihar Kogi, da ma wasu yankunan na jihar, jami’an tsaro sun bazu a sassa daban-daban na jihar domin tabbatar da tsaro.
A birnin Lokoja za a iya ganin motoci masu sulke ɗauke da jami’an sojoji da na ƴan sanda.
Gabanin zaɓen, hukumomin tsaro da dama sun yi bayanin cewa za su tabbatar an gudanar da zaɓen ba tare da tashin-tashina ba.
Kwana ɗaya gabanin zaɓen, mai taimaka wa shugaban Najeriya kan harkar tsaro, Nuhu Ribadu ya fitar da wata sanrwa inda ya ce gwamnatin ta sha alwashin daƙile duka wani yunƙuri na tayar da husuma.
A wasu wuraren kuma jami’an tsaro sun kafa shinge domin hana mutane zirga-zirga.
Rundunar ƴan sanda ta ce an hana duk wata zirga-zirga al’umma da ababen hawa waɗanda ba su zama wajibi ba daga ƙarfe 12 na daren ranar Asabar.