fidelitybank

Zaɓen Kano: An kama Mutane 288 da tayar da zaune tsaye

Date:

Rudunar ƴansandan jihar Kano, ta sanar da kama mutum 288 da take da zargi da tayar da hankalin mutane a wajen zaɓen cike gurbin majalisar jihar da ake yi, inda ta ce ta ƙwato makamai da dama a hannunsu.

A wata sanarwa da kakakin rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar, ya ce Kwamishinan ƴansandan jihar, Ibrahim Adamu Bakori ne ya jagoranci ƴansanda tare da haɗin gwiwar sauran jami’an tsaro da ke jihar wajen samun “nasarar dakile masu yunƙurin tayar da hargishin.”

“Mun fita ne domin ganin an gudanar da zaɓen cike gurbi a Ghari da Tsanyawa da Bagwai da Shanono lafiya.”

Ya ce sun samu nasarar kama mutum 288 da ake zargi ƴandaba ne masu yunƙurin tayar da zaune tsaye bisa laifuka daban-daban, sannan ya ce sun ƙwato makamai irin su adduna da bindigogin farauta da wuƙaƙe da gwafa da sauran su.

“Yanzu haka muna tsare da waɗanda muka kama, kuma da zarar mun kammala bincike, za a tabbatar an hukunta waɗanda aka tabbatar sun aikata laifi.”

nigerian 
news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp