fidelitybank

Zaɓen Kano: An kama Mutane 288 da tayar da zaune tsaye

Date:

Rudunar ƴansandan jihar Kano, ta sanar da kama mutum 288 da take da zargi da tayar da hankalin mutane a wajen zaɓen cike gurbin majalisar jihar da ake yi, inda ta ce ta ƙwato makamai da dama a hannunsu.

A wata sanarwa da kakakin rundunar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar, ya ce Kwamishinan ƴansandan jihar, Ibrahim Adamu Bakori ne ya jagoranci ƴansanda tare da haɗin gwiwar sauran jami’an tsaro da ke jihar wajen samun “nasarar dakile masu yunƙurin tayar da hargishin.”

“Mun fita ne domin ganin an gudanar da zaɓen cike gurbi a Ghari da Tsanyawa da Bagwai da Shanono lafiya.”

Ya ce sun samu nasarar kama mutum 288 da ake zargi ƴandaba ne masu yunƙurin tayar da zaune tsaye bisa laifuka daban-daban, sannan ya ce sun ƙwato makamai irin su adduna da bindigogin farauta da wuƙaƙe da gwafa da sauran su.

“Yanzu haka muna tsare da waɗanda muka kama, kuma da zarar mun kammala bincike, za a tabbatar an hukunta waɗanda aka tabbatar sun aikata laifi.”

vanguard (nigeria)

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

QPC ta nemi INEC ta soke zaɓen Kano

Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya ta nemi hukumar zaɓe...

Zaɓen Kano: An kama Mutane 288 da tayar da zaune tsaye

Rudunar ƴansandan jihar Kano, ta sanar da kama mutum...

An Kama wakilin jam’iyya da Naira miliyan 25.9 na Siyan Kuri’a

Jami’an tsaro sun kama wani da ake zargin wakilin...

Farashin kayan abinci na rugu-rugu a Najeriya – NBS

Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS) ta ce hauhawar farashin...

Kotun Kano ta ce a kamo mata Dagacin Tamburawa

Kotun Shari’ar Musulunci da ke shelkwatar Hisbah a Kano,...

Kotu ta ƙwace motocin gwamnatin Zamfara guda 40 daga hannun Matawalle

Kotun Daukaka Kara da ke a Sokoto ta tabbatar...

A na cigaba da gudanar da zaben cike gurbi harda Kano

Kano na ɗaya daga cikin jhihohin da ake kaɗa...

Mutane 12 sun mutu a wani hatsari a Kano – FRSC

Hukumar Kiyaye Haddura ta Ƙasa (FRSC) reshen Kano, ta...

Masarutar Rano ta haramta aurar da Yaran da ba su kammala karatun Firamare ba

Masarautar Rano a Kano ta haramta cire yarinya daga...

Matatar Dangote za ta fara jigilar mai kyauta ga gidajen mai

Matatar man Dangote za ta fara jigilar mai kyauta...

An sassata rikicin da aka shafe shekaru 30 kan Masallacin Sharada da Islamiyya

Tsohon dan takarar gwamnan Kano, Malam Sha’aban Ibrahim Sharada,...

Duk da kalubalen ‘yan siyasa a Kano mun shirya a zaben cike gurbi – INEC

Kwamishinan hukumar zaɓe mai zaman kanta (INEC) reshen jihar...
X whatsapp