fidelitybank

Zaɓen 2023: EFCC ta tura jami’ai 200 a Kano da Jigawa da Katsina

Date:

Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC) a ranar Juma’a ta ce, ta tura jami’an tsaro dari biyu da ke yaki da sayen kuri’u a jihohin Kano, Jigawa da Katsina a zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisar tarayya da za a yi ranar Asabar.

Kwamandan hukumar EFCC na shiyyar Kano Farouk Dogondaji ne ya bayyana haka yayin wata tattaunawa da NAN a Kano.

Dogondaji ya ce tura sojojin wani bangare ne na kudirin EFCC na tabbatar da sahihin zabe na 2023 a shiyyar.

Ya ce, “Mun tura jami’ai 50 domin sanya ido kan yadda zaben ke gudana a jihar Kano, hamsin a jihar Jigawa, hamsin kuma a jihar Katsina domin hana sayen kuri’u a duk lokacin gudanar da zabe.

“Sauran jami’ai [hamsin] an tura su zuwa filin jirgin saman Malam Aminu Kano da ke Kano da kuma filin jirgin Umaru Musa Yar’adua da ke Katsina.”

A cewar Dogondaji, hukumar na da isassun jami’an tsaro, inda ya kara da cewa a shirye suke don fuskantar duk wata barazana ko da a lokacin zabe da kuma bayan zaben.

A yau Asabar ne za a gudanar da babban zaben shekarar 2023 a fadin Jihohin Najeriya 36 ciki har da babban birnin tarayya.

cnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp