Rikicin shugabanci a jam’iyyar All Progressive Grand Alliance, APGA, ya dauki wani salo na daban, yayin da bangaren da Edozie Njoku ke jagoranta, ya sanar da rusa kwamitin gudanarwa na jam’iyyar a jihohin Kwara, Kogi, Legas, Oyo, Delta, Anambra. Jihohin Imo, Enugu, Abia da Ebonyi
Da yake jawabi ga manema labarai a Abuja, sakataren gudanarwa na jam’iyyar na kasa, Okoro Benedict, ya ce rusa kwamitocin ayyuka na jihohi goma da aka ambata ya kasance wani bangare na kokarin sasanta jam’iyyar da Njoku ke jagoranta.
Ya bayyana cewa an cimma matsayar ne bayan taron kwamitin ayyuka na kasa (NWC) wanda ya samu halartar masu ruwa da tsaki na jam’iyyar.