fidelitybank

Yunwa da ƙunci ya sa za a yi zanga-zanga a ƙasar nan – Gwamnan Oyo

Date:

Gwamna Seyi Makinde na jihar Oyo, ya bayyana cewa, fushi da yunwa da ake fama da su a fadin kasar nan ne ya sa aka shirya zanga-zangar.

Makinde ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabi a babban taron makon al’adu na Ibadan na shekarar 2024, wanda kungiyar ‘yan kabilar Ibadan ta tsakiya (CCII) ta shiryas.

An sanya ranar 1 ga watan Agusta a matsayin ranar gudanar da zanga-zangar adawa da yunwa a fadin kasar.

Makinde, yayin da yake jawabi ga mahalarta taron da aka gudanar a ranar Asabar a filin wasa na Obafemi Awolowo, Ibadan, babban birnin jihar, ya ci gaba da cewa mutane na da ‘yancin yin zanga-zanga.

Ya ce ‘yan Najeriya da ke shirin yin zanga-zangar nuna wahalhalun da ake fama da su a kasar, ya kamata su yi amfani da ‘yancinsu cikin lumana, kada su yi tashe-tashen hankula ko lalata kayayyakin jama’a.

Ya shawarci masu zanga-zangar da kada su lalata kadarorin gwamnati.

Makinde ya ce, “Najeriya na iya shiga cikin wannan hali a yanzu. Za mu iya fuskantar fushi da yunwa a cikin ƙasa don haka ne mutanenmu suke son yin zanga-zanga.

“Eh, zanga-zangar daidai ne. Amma ku tuna cewa mun yi amfani da kudinku ne wajen gina dukkan gine-gine da kayan aiki da muka sanya a jihar nan, ba nawa ba.

“Don haka, idan kuna son yin zanga-zangar, dole ne a kasance cikin lumana.

“Idan kun fara zanga-zangar ku, kada ku lalata kadarorin gwamnati, in ba haka ba, za mu yi amfani da kudaden da ya kamata mu kashe kan ayyuka masu ma’ana don maye gurbin wuraren da ka iya lalacewa.”

www.legitnews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp