fidelitybank

Yunwa da ƙunci ya sa za a yi zanga-zanga a ƙasar nan – Gwamnan Oyo

Date:

Gwamna Seyi Makinde na jihar Oyo, ya bayyana cewa, fushi da yunwa da ake fama da su a fadin kasar nan ne ya sa aka shirya zanga-zangar.

Makinde ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabi a babban taron makon al’adu na Ibadan na shekarar 2024, wanda kungiyar ‘yan kabilar Ibadan ta tsakiya (CCII) ta shiryas.

An sanya ranar 1 ga watan Agusta a matsayin ranar gudanar da zanga-zangar adawa da yunwa a fadin kasar.

Makinde, yayin da yake jawabi ga mahalarta taron da aka gudanar a ranar Asabar a filin wasa na Obafemi Awolowo, Ibadan, babban birnin jihar, ya ci gaba da cewa mutane na da ‘yancin yin zanga-zanga.

Ya ce ‘yan Najeriya da ke shirin yin zanga-zangar nuna wahalhalun da ake fama da su a kasar, ya kamata su yi amfani da ‘yancinsu cikin lumana, kada su yi tashe-tashen hankula ko lalata kayayyakin jama’a.

Ya shawarci masu zanga-zangar da kada su lalata kadarorin gwamnati.

Makinde ya ce, “Najeriya na iya shiga cikin wannan hali a yanzu. Za mu iya fuskantar fushi da yunwa a cikin ƙasa don haka ne mutanenmu suke son yin zanga-zanga.

“Eh, zanga-zangar daidai ne. Amma ku tuna cewa mun yi amfani da kudinku ne wajen gina dukkan gine-gine da kayan aiki da muka sanya a jihar nan, ba nawa ba.

“Don haka, idan kuna son yin zanga-zangar, dole ne a kasance cikin lumana.

“Idan kun fara zanga-zangar ku, kada ku lalata kadarorin gwamnati, in ba haka ba, za mu yi amfani da kudaden da ya kamata mu kashe kan ayyuka masu ma’ana don maye gurbin wuraren da ka iya lalacewa.”

nigerianewstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp