fidelitybank

Yunkurin EFCC a kotu na gurfanar da AA Zaura ya gamu da cikas

Date:

Yunkurin hukumar EFCC mai yaƙi da cin hanci da rashawa, na gurfanar da ɗan takarar sanata na jam’iyyar APC a jihar Kano, AbdulKareem AbdulSalam Zaura wanda aka fi sani da A.A Zaura kan zarge-zargen tafka damfara ya sake fuskantar cikas a kotu.

Babbar kotun tarayya da ke zamanta a Kanon ta ɗage gurfanar da A.A Zaura don bai wa sabon lauyansa dama ya je ya shirya don tunkarar shari’ar.

EFCC na zargin sa ne da damfarar wani ɗan ƙasar Kuwait kuɗi fiye da dala miliyan daya, zargin da ya sha musantawa.

Karanta Wannan: EFCC ta kama mutane 6 masu damfara ta Internet

Duk da kasancewar EFCC ta sami nasarar kawo AA Zaura gaban kotun tarayyar amma kotun ta ɗage zaman shari’ar saboda sabon sauyansa Basil Hemba bai shirya ba, inda yace yana buƙatar nazarin yadda zai tunkari batun kasancewarsa sabo kan shari’ar. iN J

Lauyar EFCC Bar. Aisha Habib ta nemi kotu ta ci gaba da sauraron shari’ar saboda ta ce sun shirya kuma sun kawo wanda ake zargin kotu, sai dai sabon lauyan AA Zaura ya ce bai shirya ba kasancewar jiya ya karɓi kunshin Shari’ar.

Wannan shi ne karo na shida da ake ƙoƙarin gurfanar da AA Zaura, amma har yanzu ba a kai ga karanto masa zarge-zargen da EFCC ke masa a gaban babbar kotun tarayyar ba.

Saboda a cewar Lauyar EFCC Bar. Aisha Habib ana ta gabatar da uzuri iri daban-daban.

Mai Shari’a Muhammad Nasir Yunusa ya ɗage zaman kotun zuwa 1 ga watan Maris, don bai wa sabon lauyan damar nazartar ƙunshin Shari’ar.

Bayanai na cewa wata babbar kotun tarayya a 2020 ta sallami AA Zaura tare da wanke shi kan da duk wani zargi da EFCC ke masa, abin da yasa EFCCn sake gabatar da zargin zamba da ake yi masa tun da farko a kotu.

vanguard (nigeria)

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...

Mukarraban gwamnati ba zan lamunci dabi’ar zubar da kima ta ba – Abba

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya gargaɗi masu...

WAEC ta sake bude shafinta don duba jarabawar bana

Hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma (WAEC) ta bayyana...

Indonesia za ta gina asibiti dubu biyu ga Falasɗinawa

Indonesia ta sanar da cewa za ta kafa wata...

Lauyan Sowore ya bukaci a sake shi cikin gaggawa

Lauyoyin ffitaccen ɗan gwagwarmayar nan kuma ɗan jarida, Omoyele...

Najeriya da Indiya za su haɗa kai na yaƙi da fataucin miyagun ƙwayoyi

Hukumar hana sha da fatauncin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya,...

Jihohi 19 da za a yi kwana 9 a na ruwan sama harda Kano – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen za a shafe kwana...

Tinubu ya mika sakon ta’aziyya bisa rasuwar matar MKO Abiola

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa bisa...

Abubuwan da Kwamiti ya gano a wajen Kwamishina mai murabus na Kano

A ranar Litinin ne kwamitin binciken badaƙalar belin Danwawu,...
X whatsapp