fidelitybank

Yunkurin EFCC a kotu na gurfanar da AA Zaura ya gamu da cikas

Date:

Yunkurin hukumar EFCC mai yaƙi da cin hanci da rashawa, na gurfanar da ɗan takarar sanata na jam’iyyar APC a jihar Kano, AbdulKareem AbdulSalam Zaura wanda aka fi sani da A.A Zaura kan zarge-zargen tafka damfara ya sake fuskantar cikas a kotu.

Babbar kotun tarayya da ke zamanta a Kanon ta ɗage gurfanar da A.A Zaura don bai wa sabon lauyansa dama ya je ya shirya don tunkarar shari’ar.

EFCC na zargin sa ne da damfarar wani ɗan ƙasar Kuwait kuɗi fiye da dala miliyan daya, zargin da ya sha musantawa.

Karanta Wannan: EFCC ta kama mutane 6 masu damfara ta Internet

Duk da kasancewar EFCC ta sami nasarar kawo AA Zaura gaban kotun tarayyar amma kotun ta ɗage zaman shari’ar saboda sabon sauyansa Basil Hemba bai shirya ba, inda yace yana buƙatar nazarin yadda zai tunkari batun kasancewarsa sabo kan shari’ar. iN J

Lauyar EFCC Bar. Aisha Habib ta nemi kotu ta ci gaba da sauraron shari’ar saboda ta ce sun shirya kuma sun kawo wanda ake zargin kotu, sai dai sabon lauyan AA Zaura ya ce bai shirya ba kasancewar jiya ya karɓi kunshin Shari’ar.

Wannan shi ne karo na shida da ake ƙoƙarin gurfanar da AA Zaura, amma har yanzu ba a kai ga karanto masa zarge-zargen da EFCC ke masa a gaban babbar kotun tarayyar ba.

Saboda a cewar Lauyar EFCC Bar. Aisha Habib ana ta gabatar da uzuri iri daban-daban.

Mai Shari’a Muhammad Nasir Yunusa ya ɗage zaman kotun zuwa 1 ga watan Maris, don bai wa sabon lauyan damar nazartar ƙunshin Shari’ar.

Bayanai na cewa wata babbar kotun tarayya a 2020 ta sallami AA Zaura tare da wanke shi kan da duk wani zargi da EFCC ke masa, abin da yasa EFCCn sake gabatar da zargin zamba da ake yi masa tun da farko a kotu.

www.leadership ng.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...
X whatsapp