fidelitybank

Youtube ya goge tashar Fasto TB Joshua

Date:

Kamfanin Youtube ya goge tashar da ke wallafa bidiyon marigayi Fasto TB Joshua saboda saba ka’idojin furta kalaman kiyayya.

Matakin ya zo makonni bayan wani bincike da BBC ta gudanar inda kungiyar Open Democracy ta bankaÉ—o shaidun cin zarafin mata da azabtarwar da marigayin ya yi a lokacin da yake raye.

Tashar Emmanuel TV ta taka rawa sosai wajen É—aga faston da ya zama fitacce a duniya.

A shekarar 2021 ne TB Joshua ya mutu sai dai cocinsa na Synagogue ya ci gaba da tafiyar da harkokinsa a karkashin mai É—akinsa Evelyn Joshua.

Har yanzu cocin bai ce komai ba kan cire tashar daga Youtube sai dai ya ƙaryata zarge-zargen da aka yi wa marigayin.

Tashar ta Emmanuel TV tana da mabiya fiye da rabin miliyan a kafar ta Youtube sannan miliyoyin mutane ne ke kallon bidiyon da tashar ke wallafawa.

Wannan ne karo na biyu cikin shekara uku da Youtube ya dakatar da tashar saboda take wasu dokokin tafiyar da tasha a Youtube.

A wani bangare na binciken da BBC, OpenDemocracy ta yi nazari kan bidiyon da tashar Emmanuel TV take wallafawa inda ta gano akwai bidiyo akalla 50 na cin zarafi a Youtube.

Tawagar kungiyar sun shigar da korafinsu kan bidiyon ga Youtube inda aka dakatar da tashar a ranar 29 ga watan Janairu.

the nation news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Yunwa na kara tsananta a arewa maso gabashin Najeriya – ICRC

Kungiyar agaji ta Red cross (ICRC) ta bayyana yadda...

Ba zan taba watsawa Tinubu kasa a ido ba – IBB

ÆŠan tsohon shugaban kasa, Janar Ibrahim Badamasi Babangida, wato...

Natasha kar ki kuskura ki dawo aiki – Majalisa

Majalisar Dattijai ta buƙaci Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta dakatar...

Za a yi ruwan sama da iska mai Æ™arfi a jihohi harda Kano – NiMET

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMET) ta fitar...

Obi da El-Rufa’i za su koma jam’iyyar mu a hukumance – ADC

Sakataren yada labarai na rikon kwarya na jam’iyyar African...

Za mu tattauna da tarayyar Turai a kan Nukiliyarmu – Iran

Iran ta tabbatar cewa za ta gudanar da tattaunawa...

Mu na gargadin Isra’ila kan korar al’ummar Gaza daga yankin su – MDD

Hukumar kula da ayyukan jin-ƙai ta Majalisar Ɗinkin Duniya...

Rikici ya kuma balle a Syria

Ƙungiyoyin kare haƙƙin dan'adam sun ce, wani sabon rikici...

Tsofaffin ‘Yansanda na da ‘yancin yin zanga-zanga – A Cewar Amnesty

Ƙungiyar Amnesty International ta ce tsofaffin ƴansandan Najeriya girmamawa...

Buhari ya yi wa Najeriya hidimar da ba za a manta da shi ba – António Guterres

Babban Sakatare na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) António Guterres...

Binani ta koma jam’iyyar haÉ—aka ta ADC

'Yartakarar gwamnan jihar Adamawa a zaɓen 2023, Sanata Aishatu...

A Talata zan koma aiki na a majalisa – Natasha

Yar majalisar Dattawa, Sanata Natasha Akpoti, ta ci alwashin...
X whatsapp