Wata motar bas ƙirar Toyota Hiace mai lamba KTG 283 XA ta ƙwace tare afka wa cikin kasuwar Damagum a jihar Yobe, inda ta hallaka wata mai juna biyu tare da wasu mutum huɗu.
Da yake tabbatar da faruwar lamarin, babban kwamandan hukumar kiyaye haɗura ta jihar, Livinus Yilzoom, ya ce hatsarin ya kuma jikkata mutum 19.
“Lamarin ya afku ne da yammaci lokacin da ake shirin rufe kasuwar. Mutane biyar ɗin da suka mutu ba su cikin motar bas ɗin, suna ƙoƙarin tsallake titi motar ta afka musu,” in ji Livinus.
Ya ce dreban motar ya yi ƙoƙarin kauce wa mutanen, amma sai motar ta ƙwace masa sannan ya afka musu.
Ya ƙara da cewa tuni aka garzaya da waɗanda suka jikkata da kuma gawawwakin waɗanda suka mutu zuwa babban asibitin Damagum.
Ya ce bincikensu ya gano cewa gudu fiye da ƙima na cikin abubuwan da suka janyo afkuwar hatsarin.