fidelitybank

Yobe: Mutane biyar sun mutu a hatsarin mota

Date:

Wata motar bas ƙirar Toyota Hiace mai lamba KTG 283 XA ta ƙwace tare afka wa cikin kasuwar Damagum a jihar Yobe, inda ta hallaka wata mai juna biyu tare da wasu mutum huɗu.

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, babban kwamandan hukumar kiyaye haɗura ta jihar, Livinus Yilzoom, ya ce hatsarin ya kuma jikkata mutum 19.

“Lamarin ya afku ne da yammaci lokacin da ake shirin rufe kasuwar. Mutane biyar ɗin da suka mutu ba su cikin motar bas ɗin, suna ƙoƙarin tsallake titi motar ta afka musu,” in ji Livinus.

Ya ce dreban motar ya yi ƙoƙarin kauce wa mutanen, amma sai motar ta ƙwace masa sannan ya afka musu.

Ya ƙara da cewa tuni aka garzaya da waɗanda suka jikkata da kuma gawawwakin waɗanda suka mutu zuwa babban asibitin Damagum.

Ya ce bincikensu ya gano cewa gudu fiye da ƙima na cikin abubuwan da suka janyo afkuwar hatsarin.

breaking news in nigeria today punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp