fidelitybank

‘Yn Najeriya na wasan buya bayan farautarsu da Trump ya ke yi

Date:

‘Yan Najeriya da ke zaune a Amurka ba da izini ba sun bayyana cewa yanzu sun takaita zirga-zirgarsu zuwa wuraren jama’a don kada a kama su a mayar da su kasarsu.

Bakin hauren sun ce sun yi haka ne bisa karfin gwiwar da suke da shi cewa za su samu kariyar fitar da su daga kasar daga tarin karar da ake shigarwa a kan Shugaba Donald Trump game da shirinsa na korar baki.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa wasu daga cikin bakin da suka tattauna da ita sun bayyana cewa sun daina zuwa aiki da coci da sauran wuraren haduwar jama’a tun bayan da aka rantsar da Trump a matsayin shugaban Amurka na 47, don gudun kada a kama su a fitar da su daga kasar.

Kamar yadda kididdigar hukumomin Amurka ta nuna akwai ‘yan Najeriya kusan 3,690 da ke fuskantar fitar da su daga kasar ta Amurka.

Mexico ce ke kan gaba da yawan wadanda za a fitar inda take da 252,044 ,sai kuma El Salvador wadda take da bakin hauren a Amurka har 203,822.

Takardun hukuma sun nuna cewa zuwa watan ranar 24 ga watan Nuwamba na 2024 akwai bakin haure 1,445,549 da za a fitar daga Amurkar.

Ma’aikatar shari’a ta Amurka ta yi barazanar gurfanar da duk kananan hukumomi ko gwamnatocin jiha da suka ki bin umarnin Shugaba Trump din na korar bakin haure.

Tun bayan da aka fara amfani da umarnin an mayar da bakin haure 538 kasashensu daga 23 ga watan Janairu.

vgn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp