fidelitybank

‘Yn Najeriya na wasan buya bayan farautarsu da Trump ya ke yi

Date:

‘Yan Najeriya da ke zaune a Amurka ba da izini ba sun bayyana cewa yanzu sun takaita zirga-zirgarsu zuwa wuraren jama’a don kada a kama su a mayar da su kasarsu.

Bakin hauren sun ce sun yi haka ne bisa karfin gwiwar da suke da shi cewa za su samu kariyar fitar da su daga kasar daga tarin karar da ake shigarwa a kan Shugaba Donald Trump game da shirinsa na korar baki.

Jaridar Punch ta ruwaito cewa wasu daga cikin bakin da suka tattauna da ita sun bayyana cewa sun daina zuwa aiki da coci da sauran wuraren haduwar jama’a tun bayan da aka rantsar da Trump a matsayin shugaban Amurka na 47, don gudun kada a kama su a fitar da su daga kasar.

Kamar yadda kididdigar hukumomin Amurka ta nuna akwai ‘yan Najeriya kusan 3,690 da ke fuskantar fitar da su daga kasar ta Amurka.

Mexico ce ke kan gaba da yawan wadanda za a fitar inda take da 252,044 ,sai kuma El Salvador wadda take da bakin hauren a Amurka har 203,822.

Takardun hukuma sun nuna cewa zuwa watan ranar 24 ga watan Nuwamba na 2024 akwai bakin haure 1,445,549 da za a fitar daga Amurkar.

Ma’aikatar shari’a ta Amurka ta yi barazanar gurfanar da duk kananan hukumomi ko gwamnatocin jiha da suka ki bin umarnin Shugaba Trump din na korar bakin haure.

Tun bayan da aka fara amfani da umarnin an mayar da bakin haure 538 kasashensu daga 23 ga watan Janairu.

vanguard news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar Æ´an Æ™asarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp