Mazauna jihar Borno dama jamiāna lafiya sun bayyana damuwa a game da karuwar yaran da basa samun abinci mai gina jiki sakamakon yunwa da iyayen da ke shayar da yaran ke fama da ita.
Rahotanni sun ce yawancin mutane da ke zaune a kananan hukumomin arewacin jihar kamar Marte da Kukawa da Abadam da Guzamala da Kaga da Mobbar da kuma Gubio sun dogara ne da kayan agajin da ake kai musu.
Da suke Magana da jaridar Daily Trust, mazauna wadannan yankuna sun bayyana matukar damuwarsu a kan tsananin yunwar da ake fama da ita sakamakon barazanar da Boko Haram ke yi musu a yankunan.
Wani mai gida da jaridar ta tattauna da shi ya ce, rashin abincin da iyaye masu shayarwa za su ci ne ke sa yaran da ake shayarwa basa samun abincin da zai gina musu jiki.
Ya ce sai iyaye mata masu shayarwa sun ci sun koshi kafin su samu ruwan nonon da zasu shayar daāyaāyansu.
Ya kara da cewa,ā Barazanar āyan Boko Haram ta tilasta mana barin ainihin muhallanmu, abin da ya sa a yanzu kullum sai mun fita domin neman abin da zamu kai wa iyalanmu su ci, ba za mu iya komawa garuruwanmu na asali ba saboda tsira da ranmu.ā
A yanzu asibitoci na cika da yaran da ke fama da karancin abinci mai gina jiki.
Duk da kokarin da kungiyar likitoci ta Medicins San Frontiers ke yi da hadin gwiwar maāaikatar lafiya wajen shawo kan wannan matsala, tallafin da ake bayarwa bai wadatarba.
Shugaban kungiyar tabbatar da adalci ta jihar Borno BOSAM, Ahmed Shehu, ya bukaci gwamnati da ta mayar da hankali wajen kirkirar abubuwan da za su rinka kare lafiya da walwalar yara a jihar. In ji BBC.