fidelitybank

Yawan yaran da ke fama da karancin abinci mai gina jiki na karuwa a Borno

Date:

Mazauna jihar Borno dama jami’na lafiya sun bayyana damuwa a game da karuwar yaran da basa samun abinci mai gina jiki sakamakon yunwa da iyayen da ke shayar da yaran ke fama da ita.

Rahotanni sun ce yawancin mutane da ke zaune a kananan hukumomin arewacin jihar kamar Marte da Kukawa da Abadam da Guzamala da Kaga da Mobbar da kuma Gubio sun dogara ne da kayan agajin da ake kai musu.

Da suke Magana da jaridar Daily Trust, mazauna wadannan yankuna sun bayyana matukar damuwarsu a kan tsananin yunwar da ake fama da ita sakamakon barazanar da Boko Haram ke yi musu a yankunan.

Wani mai gida da jaridar ta tattauna da shi ya ce, rashin abincin da iyaye masu shayarwa za su ci ne ke sa yaran da ake shayarwa basa samun abincin da zai gina musu jiki.

Ya ce sai iyaye mata masu shayarwa sun ci sun koshi kafin su samu ruwan nonon da zasu shayar da’ya’yansu.

Ya kara da cewa,ā€ Barazanar ā€˜yan Boko Haram ta tilasta mana barin ainihin muhallanmu, abin da ya sa a yanzu kullum sai mun fita domin neman abin da zamu kai wa iyalanmu su ci, ba za mu iya komawa garuruwanmu na asali ba saboda tsira da ranmu.ā€

A yanzu asibitoci na cika da yaran da ke fama da karancin abinci mai gina jiki.

Duk da kokarin da kungiyar likitoci ta Medicins San Frontiers ke yi da hadin gwiwar ma’aikatar lafiya wajen shawo kan wannan matsala, tallafin da ake bayarwa bai wadatarba.

Shugaban kungiyar tabbatar da adalci ta jihar Borno BOSAM, Ahmed Shehu, ya bukaci gwamnati da ta mayar da hankali wajen kirkirar abubuwan da za su rinka kare lafiya da walwalar yara a jihar. In ji BBC.

breaking news in nigeria today 2021

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar Ę“ansandan jihar Kaduna, sun buʙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ʙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ā€˜Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ʙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ā€˜yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp