fidelitybank

Yawan sace-sacen mutane ya karu a Najeriya – Rahoto

Date:

Wani rahoto da kamfanin Beacon Consulting da ke nazarin tsaro a Afirka ta yamma da yankin Sahel ya fitar ya nuna cewa a watan Yulin da ya gabata an samu ƙaruwar satar mutane domin kuɗin fansa a Najeriya idan aka kwatanta da Yunin wannan shekarar.

Shugaban kamfanin Dakta Kabir Adamu, ya shaida wa BBC cewa a watan Yuli kaɗai, mutum kusan 1,035 aka sace amma kuma an samu raguwa na wadanda aka kashe.

Dakta Kabiru Adamu, ya ce bisa ga mizanin da suke aunawa a watan Yunin 2024 an sace mutum 468 yayin da a watan Yuli kuma aka sace mutum 1,035.

Ya ce,” Idan aka auna za a ga kari aka samu wanda ya rubanya adadin na baya ma, to amma dangane da mace-mace kuwa an ɗan samu ragi don ba wani mai yawa bane.”

Shugaban kamfanin na Beacon Consulting, ya ce da suka yi nazari sun ga akwai abubuwan da suka janyo haka, muhimmai kuwa su ne tasirin da taɓarɓarewar tattalin arziki ke yi ga ɓangaren tsaro.

Ya ce, ” Abu na biyu kuwa shi ne siyasa,wato ‘yan siyasa na amfani da matsalar tsaron suna ƙoƙarin cimma burinsu, sai kuma abu na ƙarshe shi ne matsalar zamantakewa a tsakanin jama’a kamar shaye-shaye da suka yi tasiri a ɓangaren tsaron.”

Dakta Kabiru Adamu, ya ce wani abu da suka lura kuma shi ne masu satar mutanen sun sauya yadda suke karɓar kuɗin fansa.

Ya ce, ” A da su kan buƙaci a ba su kudade masu yawa, to amma a yanzu sun sauya salo saboda yanzu jimilar kuɗaɗe suke buƙata, ma’ana idan suka haɗa mutane da yawa sai su buƙaci a basu kudadensu a tare.

vgn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp