Mai martaba sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar III, ya ce, yau Juma’a ce 1 ga watan Sha’aban na shekarar Hijira ta 1443 a kalandar Musulunci.
Matakin ya biyo bayan ganin sabon wata da aka yi a yammacin jiya Alhamis, bayan watan Rajab ya cika kwana 29. A kalandar Musulunci, kowane wata ya na da kwana 29 amma idan ba a ga sabon wata ba za a ƙara kwana ɗaya zuwa 30. A rahoton BBC.
Hakan na nufin saura wata ɗaya cif kafin fara watan Azumin Ramadana mai tsarki. Al’ummar Musulmi kan wuni tun daga assalatu zuwa almuru ba tare da sun ci ko shan wani abu ba a Ramadana.
Da zarar an kammala Azumin Ramadana kuma sai bikin Ƙaramar Sallah ya biyo baya, wanda ake kira Eid al-Fitr.