fidelitybank

Yau ake sa ran shugaban NLC zai bayyana a ofishin ƴan sanda bisa tuhumar sa da ta’addanci

Date:

Hukumar ƴansanda  ta gayyaci shugaban ƙungiyar kwadago ta ƙasa, Joe Ajaero da ya bayyana gabanta domin amsa tambayoyi waɗanda ke alaƙa da zargin tallafa wa ta’addanci da take yi masa.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da ta fito daga ofishin mataimakin kwamishinan ƴansanda ɓangaren jami’an tattara bayanan sirri.

Sanarwar da ta samu saka hannun Adamu Muazu, jami’in yaɗa labaru na hukumar, ta ce tana kuma zargin shugaban na NLC da kutse a intanet da kuma sauran abubuwa.

Hukumar ƴansandan ta yi barazanar cewa muddin bai amsa goron gayyata da ta yi masa ba, hakan zai janyo ta kama shi.

“Ofisihinmu na binciken Ajaero kan zargin haɗa baki don aikata zamba, tallafa wa ta’addanci, cin amanar ƙasa da kuma kutse a intanet,” in ji sanarwar da ƴansandan suka fitar.

Sanarwar ƴansandan ta ƙara da cewa ana son shugaban na NLC ya bayyana ne a Talata 20 ga watan Agusta da misalin karfe 10 na safe domin amsa tambayoyi.

legit com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp