Majalisar ministocin Isra’ila ta kammala amincewa da yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza, wadda ta ƙunshi musayar waɗanda Hamas ke garkuwa da su da kuma sakin fursunoni Falasɗinawa da ake riƙe da su a Isra’ila.
Matakin na zuwa ne bayan shafe sa’o’i ana tattaunawa har zuwa cikin tsakiyar dare.
Ɗaya daga cikin ministoci masu tsattsauran ra’ayi ya ce zai ajiye muƙaminsa domin nuna adawa da batun, yayin da ɗaya kuma ya ce shi ma zai fice daga gwamnatin idan ba a ci gaba da yaƙin ba bayan ƙarewar matakin farko na yarjejeniyar, wanda zai ƙare cikin mako shida.
Yarjejeniyar za ta fara aiki ne a gobe Lahadai.
Da farko za a saki mutum uku da Hamas ke garkuwa da su yayin da ita kuma Isra’ila za ta saki Falasɗinawa fursunoni da take tsare da su.
Haka nan Isra’ila za ta fara janye dakarunta daga Gaza.