fidelitybank

Yari ya tambayi El-Rufa’ai a kan inganta lantarki idan ya zama Minista

Date:

Sanata Abdulaziz Yari ne ya yi tambayar farko, inda ya nemi sanin abin da El-Rufai zai yi don inganta samar da lantarki a Najeriya idan majalisar ta tabbatar da shi, kuma shugaba Tinubu ya naɗa shi ministan lantarki.

Sanata Karimi Sunday daga Kogi ta yamma ya ja hankalin majalisar a kan abin da ya kira ”Ƙorafi mai ƙarfi kan El-Rufai amma majalisar ba ta saurare shi ba.

Daga nan sai Sanata Khalid Ibrahim Mustapha mai wakiltar Kaduna ta Arewa ya nemi majalisar ta bari El-Rufai ya yi gaisuwa ya wuce, inda ya kafa hujja da matsayar da majalisar ta cimma a baya kan mutanen da suka taɓa zama minista ko gwamna.

Majlisar ta amince da buƙatar sanata Khalid amma ta buƙacin El-Rufai ya amsa tambayar da sanata Yari ya yi masa.

Da yake bayar da amsa, El-Rufai ya ce Najeriya tana da ƙarfin samar da lantarki ta kuma rarraba ta ga jama’ar ƙasar.

Ya ce dole a samar da sabbin kamfanonin rarraba lantarki a Najeriya don kuwa daga cikin kamfanoni 11 dake wannan aiki a yanzu uku ne kacal ke tafiyar da aikin su yadda ya kamata.

Tsohon gwamnan jihar Kadunan ya ce aikin gyara ɓangaren lantarki a Najeriya abu ne mai buƙatar haɗin gwiwar kowanne ɓangare.

www.nnn.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Luis Diaz ya zaba wa kansa makoma da ya bar Liverpool – James

Kyaftin din Colombia, James Rodríguez, ya dage cewa dan...

Ka fito ka baiwa Matawalle hakuri ko ka fuskanci fushin kotu – Shinkafi

Wani mai fafutukar kare hakkin bil’adama, Dakta Suleiman Shuaibu...

Liverpool za su sayar da ‘yan wasa uku su dauki Isak

Liverpool a shirye take ta sayar da matasan yan...

Ba zamu daga wa Hamas kafa ba har sai an saki mutanen mu – Netanyahu

Firaiministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, ya yi dogon...

Za mu gyara tsarin Maiduguri saboda ambaliya – Zulum

Gwamnan jihar Borno Babagana Umara Zulum ya ce, gwamnatinsa...

Dubban mutane sun yi zanga-zangar goyon bayan Falasɗinawa a Australia

Dubban mutane ne suka gudanar da zanga-zangar goyon bayan...

Mata da kanan Yara ne Ambaliya ta daidaita a jihohi 19 – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa, NEMA, ta...

Facebook ya ƙi amincewa da tsare-tsaren Turai na amfani da AI

Wasu muhimman tsare-tsare na dokokin Tarayyar Turai kan amfani...

Ranar 18 za a fara rajistar zabe – INEC

Hukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC ta sanar da...

Trump ya tura jiragen ruwa na yaki masu dauke da makaman nukiliya kusa da Rasha

Shugaba Trump ya ce, ya umarci a matsar da...

Amnesty na tuhumar gwamnatin Najeriya kan bacewar Dadiyata

Ƙungiyar Amnesty International ta yi Allah-wadai da sakacin da...

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...
X whatsapp