Gwamna Babajide Sanwo-Olu na jihar Legas a ranar Litinin ya yi kira ga ‘ya’yan Yarbawa maza da mata da su hada kai su marawa Sanata Bola Tinubu goyon baya.
Sanwo-Olu ya yi wannan kiran ne a bikin Ojude Oba na shekara ta 2022 a Ijebu-Ode, jihar Ogun.
Ya bukaci ‘yan kabilar Yarbawa da su mara wa Tinubu baya, tun da shi gogaggen dan siyasa ne, har ma a Afirka.
“Bari in furta cewa, a bisa tsarin hadin kan bikin Ojude Oba, babban fata na ne da kuma yakinin cewa kabilar Yarbawa za su hade a matsayin daya bayan gagarumin takarar Asiwaju Bola Ahmed Tinubu.