fidelitybank

Yaran da suka suma a kotu wasan kwaikwayo ne – Sifetan ‘Yansanda

Date:

Babban Sufeton Ƴansan kasar nan, Kayode Egbetokun ya ce, waɗanda suka suma a kotu su shida cikin waɗanda aka kai kan zargin zanga-zangar tsadar rayuwa sun yi hakan ne da gangan domin ɗaukar hankali da ɓata sunan hukumomi.

An gabatar da masu zanga-zangar ne su 114, jiya, Juma’a a wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, inda kafin gurfanar da su, huɗu daga cikinsu da suka hada da yara biyu suka faɗi, inda aka garzaya asibiti da su.

Lamarin ya ɗauki hankalin duniya tare da janyo maganganu a cikin ƙasar, inda da dama ke suka a kai.

A wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yansandan Muyiwa Adejobi ya fitar a madadin Sufet Janar ɗin, kakakin ya jadda cewa a ƙarƙashin dokokin Najeriya duk mutumin da ya kai shekarun munzalin aikta laifi, to alhakin wannan laifi da ya yi ya rataya a wuyansa ko yaya shekarunsa suke.

Sanarwar ta ce laifukan da ake tuhumar mutanen da aikatawa sun haɗa da lalata kayan gwamnati da barazana ga tsaron ƙasa da sauransu.

Alƙalin kotun ya bayar da belon kowannensu a kan naira miliyan goma da kuma mutum biyu masu tsaya wa kowanne.

legit new

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp