fidelitybank

Yaran da suka suma a kotu wasan kwaikwayo ne – Sifetan ‘Yansanda

Date:

Babban Sufeton Ƴansan kasar nan, Kayode Egbetokun ya ce, waɗanda suka suma a kotu su shida cikin waɗanda aka kai kan zargin zanga-zangar tsadar rayuwa sun yi hakan ne da gangan domin ɗaukar hankali da ɓata sunan hukumomi.

An gabatar da masu zanga-zangar ne su 114, jiya, Juma’a a wata babbar kotun tarayya da ke Abuja, inda kafin gurfanar da su, huɗu daga cikinsu da suka hada da yara biyu suka faɗi, inda aka garzaya asibiti da su.

Lamarin ya ɗauki hankalin duniya tare da janyo maganganu a cikin ƙasar, inda da dama ke suka a kai.

A wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yansandan Muyiwa Adejobi ya fitar a madadin Sufet Janar ɗin, kakakin ya jadda cewa a ƙarƙashin dokokin Najeriya duk mutumin da ya kai shekarun munzalin aikta laifi, to alhakin wannan laifi da ya yi ya rataya a wuyansa ko yaya shekarunsa suke.

Sanarwar ta ce laifukan da ake tuhumar mutanen da aikatawa sun haɗa da lalata kayan gwamnati da barazana ga tsaron ƙasa da sauransu.

Alƙalin kotun ya bayar da belon kowannensu a kan naira miliyan goma da kuma mutum biyu masu tsaya wa kowanne.

taraba state today news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...
X whatsapp