Gwamnatin Tarayya ta ce, kimanin ƴan ƙasa miliyan 61 da dubu ɗari biyar ne aka yi wa rigakafin cutar maleriya, ƙyanda, shawara, ƙyandar biri da kwayar cutar HPV mai janyo sankarar bakin mahaifa.
Hukumomi a ƙasar sun ce mafiya yawa daga cikin waɗanda aka yi wa rigakafin yara ne ƙanana.
Kuma alkaluman an tattara su ne tun daga shekarar 2023 zuwa yanzu.
Shugaban hukumar kiwon lafiya a mataki na farko na ƙasar, Muyi Aina, ya sanar da hakan a wani taron bikin makon rigakafi na Afrika da aka yi a ranar Talata a Abuja.
Inda ya ƙara da cewa aƙalla yara kusan miliyan 26 ne da ke zaune a jihohu 26 na ƙasar aka yi wa rigakafin ƙyanda a shekarar 2024.
Yayin da wasu miliyan 22 da dubu ɗari biyar da ke jihohin Borno, Yobe da kuma jihar Legas suka ƙarbi rigakafin shawara.
A ƙasar ta Najeriya ana samun ɓullar wasu cututtuka da suke shafar yara daga lokaci zuwa lokaci, waɗanda kuma a wasu lokutan kan kai ga asarar rayuka.