fidelitybank

Yara miliyan 61 sun rabauta da allurar rigakafi a Najeriya

Date:

Gwamnatin Tarayya ta ce, kimanin ƴan ƙasa miliyan 61 da dubu ɗari biyar ne aka yi wa rigakafin cutar maleriya, ƙyanda, shawara, ƙyandar biri da kwayar cutar HPV mai janyo sankarar bakin mahaifa.

Hukumomi a ƙasar sun ce mafiya yawa daga cikin waɗanda aka yi wa rigakafin yara ne ƙanana.

Kuma alkaluman an tattara su ne tun daga shekarar 2023 zuwa yanzu.

Shugaban hukumar kiwon lafiya a mataki na farko na ƙasar, Muyi Aina, ya sanar da hakan a wani taron bikin makon rigakafi na Afrika da aka yi a ranar Talata a Abuja.

Inda ya ƙara da cewa aƙalla yara kusan miliyan 26 ne da ke zaune a jihohu 26 na ƙasar aka yi wa rigakafin ƙyanda a shekarar 2024.

Yayin da wasu miliyan 22 da dubu ɗari biyar da ke jihohin Borno, Yobe da kuma jihar Legas suka ƙarbi rigakafin shawara.

A ƙasar ta Najeriya ana samun ɓullar wasu cututtuka da suke shafar yara daga lokaci zuwa lokaci, waɗanda kuma a wasu lokutan kan kai ga asarar rayuka.

general news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp