fidelitybank

Yara mata miliyan 7.6 ba sa samun damar karatu a Najeriya – UNICEF

Date:

Asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF ya bayyana cewa yara mata miliyan 7.6 a Najeriya, mafiya yawa daga yankunan arewacin kasar, ba sa samun damar karatu.

Wakiliyar UNICEF a Najeriya, Cristian Munduate ce ta bayyana hakan a gidan gwamnatin Kano yayin bikin tunawa da ranar yara mata ta duniya ta shekarar 2023 da aka yi wa taken: “Lokacinmu ne yanzu hakkinmu, makomarmu.”

Ta ce, “Yayin da nasarorin da ‘yan mata ke samu ke bayar da kwarin gwiwa ga sauran mata a wasu sassan duniya, yara mata miliyan 7.6 a Nijeriya, mafi yawa daga yankunan arewa ba sa samun wannan dama ta karatu.”

“Abin ban tsoro shi ne, Najeriya na da kashi 15 cikin 100 na yaran da ba sa zuwa makaranta a duk duniya. Amma duk da haka, kashi 9 cikin 100 na matalautan mata ne ke da damar zuwa makarantar sakandare. Wannan ba ƙididdiga ba ce kawai, kira ne na a tashi tsaye.”

“Amma ko yaya, a cikin waɗannan ƙalubalen, muna samun karin kwarin gwiwa a yau da gobe.”

Ta kara da cewa, a yayin da Kano ke matsayi na biyu a jerin ‘yan matan da ba sa zuwa makaranta a Najeriya, lamarin da ya nuna akwai tsananin banbance-banbance wajen samun ilimi, akwai bukatar a kara jaddada canjin wajen samar da ilimi.

leadership newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp