Ƙungiyar agaji ta likitoci ta Medecins Sans Frontieres MSF ta kaɗa ƙararrawa a game da abin da ta bayyana da matsananciyar yunwa da take ƙara ƙamari a yankin arewa maso yammacin Najeriya.
Ƙungiyar ta ce sama da yara 800 ne suka rasu a asibitotin da take aiki a Katsina a cikin wata tara da ta yi tana tattara bayanai a bana.
A wata ƙididdiga ta kwana-kwanan nan, an gano cewa sama da kashi na waɗanda ta duba a ƙananan hukumomi uku na jihar suna fama da matsanancin rashin abinci mai gina jiki.
Masana sun ce matsalar za ta iya ta’azzara saboda rashin kai agaji, da ƙarancin samar da abinci da ma tsadarsa.