Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar Zamfara ta haihu a birnin Madina ta Saudiyya, yayin da ake shirin gudanar da aikin Hajjin 2025.
Dandalin ƴan jarida da ke ɗauko rahotannin aikin hajji ne ya wallafa hakan a shafin sada zumutarsa na Facebook.
Rahoton ya bayyana cewa, bisa ƙa’idojin Hukumar Hajji ta Najeriya (NAHCON), ana hana mata masu juna biyu, musamman waɗanda suka kusan haihuwa tafiya aikin Hajji.
“Wannan mataki yana da nufin kare lafiyarsu da kuma kauce wa matsalolin da ka iya hana mata masu juna biyu gudanar da ibadar yadda ya kamata.” in ji rahoton.
Likitoci da hukumomin hajji na ganin cewa renon jariri na iya hana mace maida hankali da ƙarfi wajen gudanar da dukan ibadu na aikin Hajji.