Isra’ila ta kai wasu sabbin hare-hare ta sama a Gaza waɗanda rahotanni ke cewa sun yi sanadiyyar mutuwar mutane aƙalla 13.
Sojojin Isra’ila sun ce sun kai harin ne kan abin da su ka kira sansanonin sojojin Hamas.
Hare-haren baya-bayan nan na zuwa ne bayan ruwan wutar da Israi’la ta yi a daren Litinin wanda ma’aikatar lafiya da Hamas ke jagoranta ta ce ya hallaka mutum fiye da 400.
Isra’ila ta kuma rarraba takardu a wasu sassan Gaza, tana gargaɗin mutane su fice daga yankunan, ciki har da ƙauyen Beit Hanoun.
Isra’ila da Hamas dai sun sami saɓani ne kan yadda za a kai yarjejeniyar tsagaita buɗe wutar zuwa mataki na gaba bayan mataki na farko ya zo ƙarshe a farkon wannan watan.
A gefe guda kuma Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ce Isra’ila za ta cigaba da kai ”hare-hare iya ƙarfinta” kan Hamas a zirin Gaza, inda ya yi gargaɗin cewa za a cigaba da yarjejeniyar ne kawai a cikin luguden wuta, kuma ” yanzu aka fara”