fidelitybank

Yanzu mu ka fara luguden wuta a Gaza – Netanyahu

Date:

Isra’ila ta kai wasu sabbin hare-hare ta sama a Gaza waɗanda rahotanni ke cewa sun yi sanadiyyar mutuwar mutane aƙalla 13.

Sojojin Isra’ila sun ce sun kai harin ne kan abin da su ka kira sansanonin sojojin Hamas.

Hare-haren baya-bayan nan na zuwa ne bayan ruwan wutar da Israi’la ta yi a daren Litinin wanda ma’aikatar lafiya da Hamas ke jagoranta ta ce ya hallaka mutum fiye da 400.

Isra’ila ta kuma rarraba takardu a wasu sassan Gaza, tana gargaɗin mutane su fice daga yankunan, ciki har da ƙauyen Beit Hanoun.

Isra’ila da Hamas dai sun sami saɓani ne kan yadda za a kai yarjejeniyar tsagaita buɗe wutar zuwa mataki na gaba bayan mataki na farko ya zo ƙarshe a farkon wannan watan.

A gefe guda kuma Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu ya ce Isra’ila za ta cigaba da kai ”hare-hare iya ƙarfinta” kan Hamas a zirin Gaza, inda ya yi gargaɗin cewa za a cigaba da yarjejeniyar ne kawai a cikin luguden wuta, kuma ” yanzu aka fara”

daily post nigeria today news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp