Majalisar Dattawa ta fara tantance sunayen ministocin da shugaba Bola Tinubu ya mika wa zauren majalisar dokokin kasar.
A ranar Talata ne za a tantance wadanda aka nada, amma an dage atisayen zuwa ranar Laraba domin samun isasshen shiri.
A halin da ake ciki dai majalisar Dattawan ta fara tantancewar da misalin karfe 1:10 na ranar Laraba.
Dukkanin mutane bakwai da aka tantance an jera su ne a cikin takardar neman tantancewa, inda Dakta Nentawe Yilwatda daga jihar Filato ya kasance na farko.
Sauran su ne: Muhammadu Maigari Dingyadi, Bianca Odinaka Odumegwu-Ojukwu, Rt. Hon. Yusuf Abdullahi Ata, Idi Mukhtar Maiha, Dr. Jumoke Oduwole da Suwaiba Said Ahmad.