fidelitybank

‘Yansanda sun kwantar da tarzomar da ta so barkewa tsakanin Daliban marigayi Dutsen Tanshi

Date:

Kwamishinan ƴansandan jihar Bauchi, Sani-Omolori Aliyu ya yi kira ga ƴan jihar da su kwantar da hankalinsu kan hargitsin da aka samu a wani masallaicin jihar kan batun marigayi Sheikh Abdulaziz Idris Dutsen Tanshi.

A wata sanarwa da kakakin rundunar, CSP Ahmed Mohammed Wakil ya fitar, ya ce, “a ranar 4 ga Afriku ne wasu suka kai ƙarar cewa limamin masallacin Galli da ke Jahun, Ahmad Isa Jaja a cikin hudubarsa ya faɗa wasu kalamai game da Marigayi Malam Abdulaziz Idris da ba su yi wa ɗalibansa daɗi, inda suka taru a masallaci domin nuna rashin daɗinsu.”

Sanarwar ta ce hakan ya sa kwamishinan ƴansandan jihar Sani-Omolori Aliyu, ya tura jami’ai na musamman domin tabbatar da kaucewa tayar da zaune tsaye.

“Da jami’anmu suka isa masallacin, sun samu nasarar tseratar da limamin da fatattakar wadanda suka taru cikin ƙwarewa, sannan kwamishinan ƴansanda ya yi umarni a ƙaddamar da bincike domin gano musabbabin lamarin,” in ji sanarwar.

vanguard (nigeria)

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp