A yayin da ake ci gaba da takun-saka kan taron jam’iyyar PDP na kasa, NEC da ake sa ran za a yi a yau Litinin, ‘yan sanda dauke da makamai sun mamaye sakatariyar ta.
A cewar wani jami’in jam’iyyar da ya zanta da manema labarai, an tura ‘yan sanda ne domin su dakatar da taron karawa juna sani na NEC.
Duk da cewa tun farko an bar wasu ma’aikatan jam’iyyar shiga harabar sakatariyar ba tare da wata turjiya daga ‘yan sanda ba, amma daga baya aka sallame su.
A lokacin gabatar da wannan rahoto, an kuma bukaci ‘yan jarida da su fice daga harabar sakatariyar, yayin da aka ga wasu ‘yan sanda sun killace kan titin Dalaba, wanda shi ne titin da ke kan hanyar zuwa Wadata Plaza.