fidelitybank

‘Yansanda sun kashe ‘yan awaren Biafara a jihar Imo

Date:

Rundunar ‘yansandan Najeriya ta ce gamayyar jami’an tsaron ƙasar ta kashe mambobin ƙungiyar Eastern Security Network (ESN) biyar a jihar Imo da ke kudancin ƙasar.

ESN ɓangaren soji ne na ƙungiyar ‘yan’aware ta Indigenous People of Biafra (IPOB) da gwamnatin Najeriya ta haramta, wadda ke neman kafa ƙasar Biafra a kudu maso gabashin ƙasar.

Mai magana da yawun rundunar, Muyiwa Adejobi, ya faɗa ranar Lahadi cikin wata sanarwa cewa dakarun sun kashe jagororin mayaƙan biyu yayin wani samame a ranar 8 ga watan Fabarairu nan.

Sai kuma a ranar 9 ga watan dakaru suka tare wani rukunin mayaƙan dajin Nkwukwo da ke ƙaramar hukumar Mbaitoli, inda suka sake kashe wasu shugabannin uku yayin musayar wuta, a cewarsa.

Mista Adejobi ya ƙara da cewa jami’ansu sun ƙwace bindiga ƙirar AK-47 bakwai daga hannun ‘yan ƙungiyar, da bindiga harba-ruga 13, da ɗaruruwan harsasai iri-iri.

the sun newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp