Rundunar ‘yansandan Najeriya ta ce gamayyar jami’an tsaron ƙasar ta kashe mambobin ƙungiyar Eastern Security Network (ESN) biyar a jihar Imo da ke kudancin ƙasar.
ESN ɓangaren soji ne na ƙungiyar ‘yan’aware ta Indigenous People of Biafra (IPOB) da gwamnatin Najeriya ta haramta, wadda ke neman kafa ƙasar Biafra a kudu maso gabashin ƙasar.
Mai magana da yawun rundunar, Muyiwa Adejobi, ya faɗa ranar Lahadi cikin wata sanarwa cewa dakarun sun kashe jagororin mayaƙan biyu yayin wani samame a ranar 8 ga watan Fabarairu nan.
Sai kuma a ranar 9 ga watan dakaru suka tare wani rukunin mayaƙan dajin Nkwukwo da ke ƙaramar hukumar Mbaitoli, inda suka sake kashe wasu shugabannin uku yayin musayar wuta, a cewarsa.
Mista Adejobi ya ƙara da cewa jami’ansu sun ƙwace bindiga ƙirar AK-47 bakwai daga hannun ‘yan ƙungiyar, da bindiga harba-ruga 13, da ɗaruruwan harsasai iri-iri.