fidelitybank

‘Yansanda sun kama Matar da ta kashe Kishiyar ta a Bauchi

Date:

Rundunar ƴansandan jihar Bauchi ta ce, ta kama wata mata mai suna Fatima Mohammed kan zargin kashe kishiyar mai suna Hajara Isa hanyar shaƙeta a gidan mijinsu.

Cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ƴansandan jihar, Ahmed Wakil ya fitar ranar Talata ya ce tuni rundunarsu ta ƙaddamar da bincike kan lamarin.

Ya ce mijin matan – Sale Isa – ne ya kai ƙorafi wajen ƴansanda a ranar Talata.

Wakil ya ce bayan fara gudanar da bincike ƴansanda suka kama matar mai suna Fatima Mohammed mai shekara 28, wadda daga baya ta amsa laifinta a lokacin ƴansanda suke tuhumarta.

“A lokacin da ake tuhumarta ta amsa laifinta inda tace shaƙe kishiyartata ta yi, har sai da ta mutu”, in ji sanarwar.

Sanarwar ta ƙara da cewa ”bayan ta kashe ta, ta yi ƙoƙarin yin ɓadda-bami, ta yadda ba za a zarfgeta ba, inda ta watsa mata ruwan zafi, sanna ta ƙonata da wasu buhun da ya fara lalacewa”.

Tuni dai aka mayar da binciken ofishin kula da manyan laifuka da ke jihar domin faɗaɗa bincike.

A baya-bayan nan jihar Bauchi na fuskantar matsalolin kisan kai, wani da ke ƙara haifar da fargaba.

A farkon makon nan ma an kama wani matash bisa zargin kashe mahaifiyarsa, bayan da a farkon azumi aka zargi wani miji da kashe matarsa.

www.nnn.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...
X whatsapp