fidelitybank

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Date:

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il da aka fi sani da Linga ɗan Unguwar Dala, tare da abokinsa Sani Abdulsalam da aka fi sani da Guchi, bisa zargin yada bidiyo suna rike da makamai a TikTok da sauran kafafen sada zumunta.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawunta, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya fitar a ranar Laraba, 27 ga watan Agusta, 2025.

A cewar sanarwar, an samu takobi guda ɗaya da sanduna biyu a hannunsu, inda ake zargin suna amfani da bidiyo a shafukan TikTok da Facebook wajen tsoratar da jama’a, abin da ke tada hankulan al’umma.

Kwamishinan ’yan sandan Kano, Ibrahim Adamu Bakori, ya ce an kaddamar da cikakken bincike kan lamarin, tare da gargadin cewa duk wanda aka kama yana yaɗa bidiyo rike da makamai ko ya shiga harkar ’yan daba, za a gurfanar da shi a kotu.

Rundunar ta kuma yi kira ga iyaye su ja hankalin yaransu kan guje wa irin waɗannan ayyuka, tare da tabbatar da cewa za su ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin al’umma a jihar.

nnn.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...

A sake sabon tsarin shugabancin INEC a Najeriya – Goodluck

Tsohon shugaban kasa, Goodluck Jonathan, ya yi kira da...

Magoya bayan West Ham ku hada kai da Bowen – Potter

Mai horas da West Ham, Graham Potter ya bukaci...

Alhaki na ne kifewar jirgin kasa – Shugaban Hukumar

Shugaban hukumar jiragen ƙasa ta Najeriya (NRC), Kayode Opeifa,...

Tinubu ya haramta fitar da ɗanyen man kaɗanya

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya bayar da umarnin dakatar...

Hisba ta karɓi ƙorafe-ƙorafe 83,776 a Kano

Rundunar Hisbah ta jihar Kano ta bayyana cewa, a...

Ganduje ba dan cin hanci ba ne – Martanin Garba Ga Gwamnatin Kano

Tsohon kwamishinan yaɗa labarai na Jihar Kano, Muhammad Garba,...

Kungiyar Malaman Jami’o’i bangaren BUK sun yi zanga-zangar Lumana

Kungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU), reshen Jami’ar Bayero Kano (BUK),...

An gargadi Borno da Yobe da Jigawa su zama cikin shirin ambaliya

Akwai yiwuwar samun ambaliya a jihohin Borno, Jigawa da...
X whatsapp