fidelitybank

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Date:

Tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam’iyyar LP, Peter Obi, ya bukaci rundunar ƴansandan Najeriya ta gaggauta sakin ɗan fafutikar nan Omoleye Sowore ko ta gurfanar da shi a gaban kotu.

Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X, Mista Obi ya bayyana damuwarsa kan matakin da ƴansandan suka ɗauka na ci gaba da tsare Sowore.

”Ina mamakin yadda za a ci gaba da tsare mutumin da ya kai kansa domin amsa gayyatar da ƴansanda suka yi masa”, in ji shi.

Mista Obi ya ce ɗabi’ar da ƴansandan Najeriya ke nunawa ta fara rusa kyakkyawan fatan da ƴan Najeriya ke da shi kan rundunar ƴansandan.

A ranar Laraba ne rundunar ƴansanda Najeriya ta tsare Sowore bayan ya amsa gayyatar da rundunar ta yi masa domin amsa wasu tambayoyi.

Lauyoyinsu sun yi zargin cewa ana ci gaba da tsare shi yanayi na muzgunawa da cin zarafi.

Tuni dai ƙungiyoyin kare hakkin bil’adama a Najeriya suka fara kiraye-kirayen a sake shi

legit news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

INEC za ta bai wa ɗaurarru damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓuka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

Ɗaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaɗi mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaɗi...

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...

Mukarraban gwamnati ba zan lamunci dabi’ar zubar da kima ta ba – Abba

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya gargaɗi masu...

WAEC ta sake bude shafinta don duba jarabawar bana

Hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma (WAEC) ta bayyana...

Indonesia za ta gina asibiti dubu biyu ga Falasɗinawa

Indonesia ta sanar da cewa za ta kafa wata...
X whatsapp