Wasu rahotanni na cewa ‘yanbindiga sun sace wani sabon kansila da kuma mutum takwas a yankin ƙaramar hukumar Kabba-Bunu da ke jihar Kogi a yankin arewa maso tsakiyar Najeriya.
Jaridar Vanguard ta ruwaito cewa ‘yanbindigar sun kai hari ne a cikin daren da ya gabata da misalin ƙarfe 1:00, inda suka sace mutanen daga gidajensu, ciki har da sabon kansilan da ke wakiltar mazaɓar Odo-Ape Hon. Alaba Ope.
Wani da ya ga yadda lamarin ya faru, wanda ya buƙaci a ɓoye sunansa ya ce ‘yanbindigar sun buɗe wuta ne da suka shiga garin da misalin ƙarfe ɗaya na dare, kafin su bi gida-gida su kamo waɗanda suka yi garkuwa da su.
Kusan mako uku baya, aka sace mutum uku da suka haɗa da wani yaro mai shekara takwas a garin.
Jaridar ta ce ta kakakin ‘yansanda na jihar SP William Anya, bai bayar da amsar saƙon da ta aika masa ba na samun bayani game da lamarin, amma ta ce wani babban jami’in tsaro na gwamnati ya tabbatar mata da labarin.