fidelitybank

‘Yanbindiga sun sace Kansila da wasu mutune 8 a jihar Kogi

Date:

Wasu rahotanni na cewa ‘yanbindiga sun sace wani sabon kansila da kuma mutum takwas a yankin ƙaramar hukumar Kabba-Bunu da ke jihar Kogi a yankin arewa maso tsakiyar Najeriya.

Jaridar Vanguard ta ruwaito cewa ‘yanbindigar sun kai hari ne a cikin daren da ya gabata da misalin ƙarfe 1:00, inda suka sace mutanen daga gidajensu, ciki har da sabon kansilan da ke wakiltar mazaɓar Odo-Ape Hon. Alaba Ope.

Wani da ya ga yadda lamarin ya faru, wanda ya buƙaci a ɓoye sunansa ya ce ‘yanbindigar sun buɗe wuta ne da suka shiga garin da misalin ƙarfe ɗaya na dare, kafin su bi gida-gida su kamo waɗanda suka yi garkuwa da su.

Kusan mako uku baya, aka sace mutum uku da suka haɗa da wani yaro mai shekara takwas a garin.

Jaridar ta ce ta kakakin ‘yansanda na jihar SP William Anya, bai bayar da amsar saƙon da ta aika masa ba na samun bayani game da lamarin, amma ta ce wani babban jami’in tsaro na gwamnati ya tabbatar mata da labarin.

the sun newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...
X whatsapp