‘Yan wasa 16 sun yi atisaye a ranar Talata yayin da Super Eagles ta fara shirye-shiryen tunkarar wasannin sada zumunta da za ta yi da Ghana da Mali.
Fitattun taurari kamar su Ademola Lookman, Alex Iwobi, Calvin Bassey, Moses Simon, Semi Ajayi da Stanley Nwabali na cikin ‘yan wasan da suka riga mu gidan gaskiya.
Ana sa ran sauran ‘yan wasa shida za su hadu da takwarorinsu a sansanin ranar Laraba (yau).
‘Yan wasan su ne Wilfred Ndidi da Frank Onyeka da Kelechi Iheanacho da Chidozie Awaziem da Bright Osayi-Samuel da kuma Francis Uzoho .
Tawagar Super Eagles na da sansaninta ne a otal din Adam Park da ke Marrakech.
Yan wasa 16 a sansanin sune:
Stanley Nwabali, Ojo Olorunleke, Jamilu Collins, Bruno Onyemaechi, Semi Ajayi, Calvin Bassey, Benjamin Tanino
Alhassan Yusuf, Alex Iwobi , Fisayo Dele -Bashiru, Raphael Onyedika
Ademola Lookman, Moses Simon, Cyriel Dessers, Sadiq Umar, Nathan Tella
YAN WASAN DA AKE SARAN
Wilfred Ndidi, Frank Onyeka, Francis Uzoho, Bright Osayi-Samuel, Kelechi Iheanacho, Chidozie Awaziem