fidelitybank

‘Yan waje na zuwa Najeriya neman lafiya – Dr Tunji

Date:

Gwamnatin Tarayya ta ce, tsarin kula da lafiyar kasar nan ya janyo hankalin marasa lafiya na kasashen waje, ciki har da Indiya zuwa neman magani a Najeriya.

A wata hira da aka yi da shi a gidan talabijin na Arise a ranar Litinin, karamin ministan lafiya, Dakta Tunji Alausa, ya yi ikirarin cewa, har yanzu harkar kiwon lafiyar kasar ba ya cikin wani mawuyacin hali.

Ya yi iƙirarin cewa tare da ingantuwar tsarin kiwon lafiya, ƙasar nan na samun tagomashi, ta yadda ma’aikatan lafiya na dawowa gida daga ketare su aiwatar da aikin lafiya a kasar nan.

Ministan ya yi nuni da cewa Najeriya ta zama kasar da aka fi son zuwa yawon bude ido a bangaren lafiya, musamman ma hanyoyin tiyata, wanda ya fi tsada idan aka kwatanta da sauran kasashe.

A cewarsa, yawaitar asibitocin gyaran kashi da ya kai kusan 900 a fadin kasar nan, ya kuma taimaka wajen jawo hankalin marasa lafiya da ke neman ayyuka kamar aikin tiyata.

Ya yi nuni da cewa kudurin gwamnatin na ba da fifiko ga lafiyar jama’a ya haifar da sauye-sauye masu kyau a bangaren kiwon lafiya.

Ya kara da cewa gwamnati ta ware kudade da aka sadaukar tare da bullo da hadin gwiwa, domin inganta ayyukan kiwon lafiya a matakin farko da fadada inshorar lafiya

nigeria.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp