Ƙungiyoyi ‘yantawayen Syria na dannawa zuwa Damascus, babban birnin ƙasar daga arewaci da kudancin ƙasar, yayain da dakarun soji ke ci gaba da rasa yankunan da ke hannunsu.
Rahotonni daga lardin Daraa da ke kudancin ƙasar sun ce ‘yantawayen sun ƙwace iko da lardin, bayan da sojojin gwamnati suka fice daga lardin bisa alƙawarin ba su damar janyewa.
Bayanai da ke shigowa a yanzu sun nuna cewa a yanzu ‘yantawayen da suka danno daga kudancin ƙasar suna tazarar kilomita 10 aga birnin.
A can ma yankin arewacin babban birnin, ƙungiyar IS da ke jagarantar tawayen sun ƙaddamar da hari kan birnin Homs.
Bayanai na cewa ‘yantawayen sun ƙwace iko da birnin Quneitra da ke kusa da tuddan Golan da ke kusa da kan iyakar ƙasar da Isra’ila. In ji BBC.