fidelitybank

‘Yan takara ku amince da sakamakon zaben 2023 – Kungiyar Kiristoci

Date:

Kungiyar kiristoci ta kasa CAN, ta shaidawa daukacin jam’iyyun siyasa da ‘yan takararsu cewa, dole ne su kasance a shirye su amince da sakamakon zaben shugaban kasa da sauran zabuka ko da irin wannan sakamako bai yi masu ba.

Kungiyar ta CAN ta kuma dage kan cewa dole ne hukumar zabe ta kasa INEC ta sanya dukkan matakan da suka dace a wannan lokaci domin baiwa ‘yan Najeriya sahihin zabe.

Kungiyar ta CAN ta bayyana haka ne a cikin wata sanarwa dauke da sa hannun shugabanta, Archbishop Daniel C. Okoh, kuma ta mika wa manema labarai a Abuja ranar Juma’a.

Kungiyar ta CAN ta bayyana karara cewa zabe ba yaki ba ne, don haka ya kamata a kalli lokacin mika mulki cikin lumana.

Dangane da batun tsaro, kungiyar kiristoci ta yi kira ga hukumomi da su sanya na’urorin da suka dace, musamman a cikin al’ummomin da ke fuskantar hare-hare tare da tabbatar da cewa babu wani dan kasa da aka tauye hakkinsa saboda tabarbarewar tsaro a sassan kasar.

“[Muna] kira ga dukkan jam’iyyun siyasa da ‘yan takara masu neman mukamai a lokacin babban zabe mai zuwa da su amince da sakamakon zabe da gaskiya domin amfanin ‘yan Najeriya da hadin kan kasar,” in ji CAN.

tribune news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Hogan ya mutu bisa cutar gazawar koda

An bayyana cikakkun bayanai game da mutuwar ɗan wasan...

Sojoji sun kashe rikaken dan Bindiga Dan Dari Biyar a Sokoto

Dakarun Operation FANSAR YANMA sun yi nasarar fatattakar wani...

An kashe utane 30 a yakin Thailand da Cambodia

An shiga kwana na uku na faɗan kan iyaka...

Ba mu ƙayyade shekarun shiga ƙaramar sakandare JSS1 – Ma’aikatar Ilimi

Ma'aikatar Ilimi a Najeriya ta musanta rahoton da wasu...

Ido da Ido na ga yadda Sojojin Isra’ila ke kashe Falasdinawa – Tsohon Sojin Amurka

Wani tsohon sojan Amurk ya ce, ya ga yadda...

‘Yan majalisar Birtaniya 220 na neman ƙasar ta amice da ƙasar Falasɗinu

'Yan majalisar Birtaniya 220 sun nemi gwamnatin ƙasar ta...

Buhari yaki karbar kyautar Agogon lu’u-lu’u da jirgin sama – Garba Shehu

Mai magana da yawun tsohon Shugaban Najeriya Muhammad Buhari,...

An kama wanda ya kashe tsohuwar Matarsa a Jigawa

Ƴansandan Jihar Jigawa sun ce, sun kama wani mutum...

Fadar shugaban kasa ta mayar da martani kan Kwankwaso

Fadar shugaban kasa, ta mayar wa tsohon gwamnan Kano...

Barau FC ta naɗa Ladan Bosso sabon kocinta

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barau FC ta sanar da...

Am fara dawo da ‘yan Najeriya daga Afrika ta Tsakiya

Hukumomi a Najeriya sun ce, sun fara ƙoƙarin mayar...

G-Fresh da Hamisu Breaker sun samu gurbi kurkuku bayan sun watsa Naira

Babbar kotun tarayya da ke jihar Kano ɗaure shahararrun...
X whatsapp