fidelitybank

‘Yan takara ku amince da sakamakon zaben 2023 – Kungiyar Kiristoci

Date:

Kungiyar kiristoci ta kasa CAN, ta shaidawa daukacin jam’iyyun siyasa da ‘yan takararsu cewa, dole ne su kasance a shirye su amince da sakamakon zaben shugaban kasa da sauran zabuka ko da irin wannan sakamako bai yi masu ba.

Kungiyar ta CAN ta kuma dage kan cewa dole ne hukumar zabe ta kasa INEC ta sanya dukkan matakan da suka dace a wannan lokaci domin baiwa ‘yan Najeriya sahihin zabe.

Kungiyar ta CAN ta bayyana haka ne a cikin wata sanarwa dauke da sa hannun shugabanta, Archbishop Daniel C. Okoh, kuma ta mika wa manema labarai a Abuja ranar Juma’a.

Kungiyar ta CAN ta bayyana karara cewa zabe ba yaki ba ne, don haka ya kamata a kalli lokacin mika mulki cikin lumana.

Dangane da batun tsaro, kungiyar kiristoci ta yi kira ga hukumomi da su sanya na’urorin da suka dace, musamman a cikin al’ummomin da ke fuskantar hare-hare tare da tabbatar da cewa babu wani dan kasa da aka tauye hakkinsa saboda tabarbarewar tsaro a sassan kasar.

“[Muna] kira ga dukkan jam’iyyun siyasa da ‘yan takara masu neman mukamai a lokacin babban zabe mai zuwa da su amince da sakamakon zabe da gaskiya domin amfanin ‘yan Najeriya da hadin kan kasar,” in ji CAN.

newstoday

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp