Bulaliyar majalisar dattawa kuma tsohon gwamnan jihar Abia, Sanata Orji Uzor Kalu, ya yi ikirarin cewa, ‘yan takarar shugabancin kasa guda tara na jam’iyyar APC na shirin marawa shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan.
Da yake magana da manema labarai a ranar Asabar din da ta gabata, tsohon dan takarar shugaban kasa ya ce, dan takarar shugaban kasa daga jam’iyyar PDP shi ma zai koma APC.
Orji Kalu, wanda ya yi watsi da aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban kasa kuma ya goyi bayan na Lawan, ya bayyana cewa takarar shugaban majalisar dattawa za ta yi ‘kara kamar guguwa.
Ya ce: “Batun dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC za a warware tun kafin zaben fidda gwani.
“Yayin da nake magana da ku, kimanin ‘yan takarar shugaban kasa tara daga jam’iyyarmu ne suka sanar da ni shirinsu na janye aniyarsu ta tsayawa takarar shugaban kasa na marawa Ahmad Lawan baya.