Kimanin ‘yan takara 700 da suka fafata a zaben fidda gwani na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) na neman tikitin takarar majalisar wakilai, sun yi alkawarin baiwa dan takarar jam’iyyar Asiwaju Bola Ahmed Tinubu kuri’u da bai gaza miliyan uku ba.
Tsoffin ‘yan takarar wadanda wasu daga cikinsu ‘yan majalisar ne, sun kuma yi alkawarin goyon bayan ‘yan takarar jam’iyyar a zabukan gwamnoni da na majalisun tarayya da na majalisun jiha.
Shugaban kungiyar ‘yan takarar majalisar wakilai Alphonsus Komsol Longapp, wanda ya yi magana a lokacin da yake kaddamar da taron a Abuja, ya ce ‘yan takarar 700 na da karfin tattara kuri’u da bai gaza 4500 ba daga mazabu 360 na tarayya a fadin kasar nan don neman dan takarar jam’iyyar APC.
Longapp ya ce nasarorin da gwamnatin Buhari ta samu a cikin shekaru bakwai da rabi ba za a bar su a hannun wadanda suka durkusar da kasar nan tsawon shekaru 16 ba.
Dandalin dai ya kunshi dukkan masu neman kujerar majalisar wakilai ta APC ta tarayya da suka halarci zabukan fitar da gwani na jam’iyyar.