Rahotanni daga garin Ɗan Gulbi cikin jihar Zamfara, sun ce ‘yan fashin daji sun far wa mutane da harbi a gonakinsu.
Shaidu sun ce an kashe sama da mutum 10 tare da jikkata wasu.
Harin na ƙaramar hukumar Maru na zuwa ne kwana biyu, bayan da ‘yan fashin daji su ka yi wa mutum biyar yankan rago a ƙauyen Kango.
Kwamishinan tsaro na jihar ya bayyana harin a matsayin mummunan labari amma yana jiran cikakken bayani.