Wasu ‘yan ta’adda sun yi garkuwa da wata mata da diyarta da wani direban dan kasuwa da ke kai su Kaduna bayan wani aikin jin kai da raba kayayyakin ga marasa galihu a yankin Mariri da ke karamar hukumar Lere ta jihar.
Wata majiya ta shaida wa manema labarai a jiya, a Kaduna, cewa mamacin mai suna Ramatu Abarshi, Injiniya da diyarta suna komawa Kaduna, bayan ziyarar da suka kai kauyen Mariri da ke karamar hukumar Kajuru, inda suka raba kayan gida ga marasa galihu kafin bukukuwan Sallah.
A cewarsa, bayan ta raba kayan ne, kuma tana komawa Kaduna ne ‘yan ta’addan suka tare motar da suka yi haya ta kasuwanci suka yi garkuwa da su a wani kauye da ke kusa da Kasuwan Magani.
“Ta zo ne don raba tufafi da sauran kayan yau da kullun ga marayu gabanin bikin Eid-el-Fitr.
Majiyar ta kara da cewa, “Ta yi musabaha da mutane da dama a Mariri tare da daukar hotuna da mutane da dama kafin su tafi da yamma.”
A cewarsa, a wani wuri tsakanin ‘Crossing da Kasuwan Magani,’ an yi zargin ‘yan bindiga ne suka kai wa motar su hari, inda suka yi awon gaba da su ciki har da direban motar.
Wani abokin dangin wanda aka sace shi ma ya shaida wa manema labarai cewa, barayin sun yi martani tare da neman Naira miliyan 100, domin a sako Ramatu da diyarta.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Kaduna, Mataimakin Sufeto Mohammed Jalige, bai tabbatar da faruwar lamarin ba har ya zuwa lokacin da aka buga waya domin bai amsa kiran wayar da aka yi masa ba.