fidelitybank

‘Yan ta’adda sun yi garkuwa da mutane 63 a Neja

Date:

‘Yan ta’adda sun yi garkuwa da mutane 63 a garuruwan Durmin, Jarmiya, da Pandogari da ke karamar hukumar Rafi a jihar Neja.

An sace akalla mutane 41 daga Durmin, mutane 14 daga Jarmiya da kuma mutane takwas daga Pandogari.

Wata majiya ta ce daga cikin mutane 14 da aka yi garkuwa da su a Jarmiya, takwas an sake su ne bayan da ‘yan ta’addan suka karbi Naira miliyan 6 da babura biyu a matsayin kudin fansa.

Sauran shidan kuma, ‘yan ta’addan na neman naira 200,000 da suka rage domin a sake su.

A Durmin ‘yan ta’addan sun karbi Naira miliyan 8 daga iyalan mutane takwas da suka yi garkuwa da su yayin da wasu 33 ke hannun su.

Haka kuma, rundunar hadin gwiwa ta jami’an tsaro a Nijar ta ceto mutane 13 da aka sace a karamar hukumar Gurara.

A wata sanarwa da kwamishinan tsaro na cikin gida da ayyukan jin kai, Emmanuel Umar ya fitar, ya ce an kubutar da wadanda harin ya rutsa da su ne bayan da jami’an tsaro suka kai samame yankin.

hausa news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...
X whatsapp