fidelitybank

‘Yan ta’adda sun sace Basarake a Abuja

Date:

Wasu yan bindiga dauke da makamai sun sace mai unguwar Kuchibiyu da ke Kubwa, ƙaramar hukumar Bwari a babban birnin Tarayyar Abuja.

Wata majiya a unguwar ta ce an sace Malam Isiaka Dauda ne a cikin gidansa, mitoci kaɗan zuwa fadarsa, lokacin harin wanda aka fara kai wa tun daga sha biyu na dare zuwa daya na dare.

Ya ce, ƴan bidigar da yawansu ya kai goma, sun yi harbi sau biyu bayan zuwansu, abun da ya jfa fargaba a zukatan mutan.

Ya ƙara da cewa da farko maharan sun danna wani ɗaki ne da suka samu basaraken a ciki.

‘’Sun tafi da shi ba tare da tirjiya ba, ta wata hanya marar kyau suka bi suka ɓulle suka tafi’.

Har kawo yanzu dai masu garkuwar ba su buƙaci komai ba tukuna.

Babban jami’in ƴan sandan yankin Kubwa ACP Muhammad Ndagi wanda ya tabbatar da aika-aikar ya ce, za su yi bincike a kan al’amarin.

Wannan na faruwa ne watanni uku bayan yin garkuwa da mai unguwar Bukle da ke yankin Kwali a Abujan Alhaji Hassan Shamisozhi a fadar shi. In ji BBC.

An sake shi bayan shafe kwanaki goma sha takwas a hannun masu garkuwar.

naija hausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...

Mun samu kuɗin gina titin jirgi daga Maiduguri zuwa Abia – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ce, ta samu duka kuɗin gudanar...

Sanatocin Arewa sun yi tir da kisan Zamfara

Ƙungiyar sanatocin Arewa, ta yi Allah wadai da kisan...

Tattalin arzikin Najeriya zai kara bunkasa a shekarar nan – IMF

Asusun Bayar da Lamuni na Duniya, IMF ya sabunta...

Ma’aikatan jinya sun fara yajin aiki a Najeriya

Ƙungiyar ma'aikatan jinya da unguzomomi ta kasa, ta fara...

Birtaniya ta na tsantsanr goyon bayam Hamas ne kawai – Netanyahu

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, matakin da Birntaniy...

Birtaniya ta gindaya wa Isra’ila sharuɗa

Firaministan Birtaniya, Keir Starmer, ya shimfiɗa wa Isra'ila wasu...
X whatsapp