fidelitybank

‘Yan ta’adda sun kashe ‘yan sanda 5 da fararen hula 3 a Katsina

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Katsina, ta tabbatar da kashe jami’an ‘yan sanda biyar da wasu fararen hula uku a karamar hukumar Kankara da ke jihar.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, SP Isah Gambo, ya tabbatar wa manema labarai faruwar lamarin a Katsina, inda ya ce mutane takwas ne suka rasa rayukansu a harin wanda aka kai da misalin karfe 6:30 na yammacin ranar Laraba.

A cewarsa, wadanda harin ya rutsa da su sun hada da ‘yan sanda biyar da farar hula uku, inda ya ce jami’an ‘yan sandan sun fito ne daga rundunar ‘yan sandan jihar Kano da ke gudanar da ayyuka na musamman a yankin.

‘Yan ta’addan wadanda yawansu ya haura 200 a kan babura, dauke da bindigogi kirar AK-47, da dai sauransu, an ce sun kai harin ne a kauyen Gatikawa da ke karamar hukumar Kankara da misalin karfe 6:30 na yammacin ranar Laraba.

An ce sun shafe sama da sa’a guda suna gudanar da aikinsu, inda suke tafiya gida gida, suna wawashe kayan abinci, kudi, da sauran kayayyaki masu daraja.

Gambo, ya ci gaba da cewa, ana ci gaba da gudanar da bincike domin bankado lamarin.

nnn.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp