A kalla rayuka 18 ne suka salwanta a kauyen Kadaddaba da ke karamar hukumar Anka a jihat Zamfara a wani sabon farmakin da ‘yan ta’adda suka kai yankin.
Mazauna yankin sun ce ‘yan ta’addar sun kwashe sa’o’i shida suna barin wuta, inda suka bi gida-gida tare da kwace abinci, kudi da dabbobi.
Rahotanni sun tabbatar da cewa, wadanda suka yi yunkurin barin garin ko kuma masu taurin kai ne ‘yan ta’addan suka halaka.
A cewar Premium Times, farmakin ya kwashe kusan sa’o’i hudu ‘yan ta’addan suka bayyana wurin karfe goma na dare, kuma suka kai har hudun asuba kuma shi ne na farko da aka taba kai wa kauyen.