fidelitybank

‘Yan ta’adda sun hallaka mai juna biyu da mata hudu a Naija

Date:

Ƴan ta’adda sun hallaka wata mata mai juna biyu na wata shida da wasu mutum huɗu a garin Agwa da ke ƙaramar hukumar Rafi ta jihar Naija.

Haka kuma ‘yan ta’addar sun sace kusan mutum 50 da raunata wasu a hare-haren da suka kai jiya Talata a yankin ƙaramar hukumar ta Rafi da kuma Wushishi kamar yadda jaridar Vanguard.

Rahotanni sun ce maharan sun riƙa harbin kan mai-uwa-da-wabi a lokacin da suka kai farmakin, sai dai sojoji sun katse musu hanzari inda suka farmake su da hari ta sama.

Karanta Wannan: Obi ya jagoranci tawagar Lauyoyinsa zuwa kotu

Duk da cewa sojojin sun kore su to amma ƴan bindigar sun yi awon-gaba da mutum aƙalla 50, yawanci yara da mata kamar yadda bayanai suka nuna.

Al’ummar yankin da abin ya faru na nuna fargaba kan tsaronsu yayin da ake shirin zaɓen gwamna da ƴan majalisar dokokin jiha ranar Asabar.

Kwamishinan tsaro da ayyukan jin-ƙai na jihar, Emmanuel Umar, wanda ya tabbatar da kai harin zuwa lokacin bayyana labarin, ya ce ba su tantance yawan mutanen da lamarin ya rutsa da su ba.

breaking news in nigeria today 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp