fidelitybank

‘Yan ta’adda sun hallaka mai juna biyu da mata hudu a Naija

Date:

Ƴan ta’adda sun hallaka wata mata mai juna biyu na wata shida da wasu mutum huɗu a garin Agwa da ke ƙaramar hukumar Rafi ta jihar Naija.

Haka kuma ‘yan ta’addar sun sace kusan mutum 50 da raunata wasu a hare-haren da suka kai jiya Talata a yankin ƙaramar hukumar ta Rafi da kuma Wushishi kamar yadda jaridar Vanguard.

Rahotanni sun ce maharan sun riƙa harbin kan mai-uwa-da-wabi a lokacin da suka kai farmakin, sai dai sojoji sun katse musu hanzari inda suka farmake su da hari ta sama.

Karanta Wannan: Obi ya jagoranci tawagar Lauyoyinsa zuwa kotu

Duk da cewa sojojin sun kore su to amma ƴan bindigar sun yi awon-gaba da mutum aƙalla 50, yawanci yara da mata kamar yadda bayanai suka nuna.

Al’ummar yankin da abin ya faru na nuna fargaba kan tsaronsu yayin da ake shirin zaɓen gwamna da ƴan majalisar dokokin jiha ranar Asabar.

Kwamishinan tsaro da ayyukan jin-ƙai na jihar, Emmanuel Umar, wanda ya tabbatar da kai harin zuwa lokacin bayyana labarin, ya ce ba su tantance yawan mutanen da lamarin ya rutsa da su ba.

legitnews.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...

Isra’ila ta buga gangar yaƙi – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei, ya ce...

Iran ta na cigaba da luguden makami mai Linzami cikin Isra’ila

Ana ci gaba da zaman dar-dar a Isra'ila yayin...

Alhazan Najeriya sun fara dawo wa daga ƙasar Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da isowar...

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...
X whatsapp