Gwamnatin tarayya ta yi nadamar yadda ake ci gaba da barnata ababen more rayuwa, lamarin da ke shafar karfinta na isar da wutar lantarki, inda ta ce, a yanzu gwamnati na yaki da ‘yan ta’adda domin dawo da aikin.
Ministan Wutar Lantarki, Abubakar Aliyu ne ya bayyana hakan a ranar Larabar da ta gabata yayin da yake zantawa da manema labarai sakamakon taron majalisar zartaswa ta tarayya da mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo ya jagoranta a fadar shugaban kasa da ke Abuja.
Da ya ke ba da misali da yankin Arewa maso Gabas da Arewa maso Yamma da kuma Arewa ta Tsakiya, ya ce, bayan da ‘yan barna suka durkusar da samar da wutar lantarki aka mayar da su sai su sake lalata su.
Ya ce, a yanzu an tilasta wa gwamnati ta tsara wasu hanyoyi daban-daban, amma marasa inganci don samar da wutar lantarki a yankunan da abin ya shafa musamman Maiduguri a jihar Borno.
Ministan ya kuma ce, jami’an sa ba su samu damar shiga ayyukan samar da wutar lantarki da aka lalata a jihar Neja ciki har da Shiroro domin sanin matsalarsu saboda rashin tsaro a yankin.
Sai dai ya ce, hukumomin tsaro na ba ma’aikatarsa hadin kai kan yadda za a shawo kan lamarin.
Da yake magana kan daya daga cikin irin wadannan ayyuka da FEC ta amince da shi ya bayyana cewa: “Sai na shida a Damaturu Jihar Yobe. Wannan shi ne na musamman domin kamar yadda ku ka sani, sama da shekara guda Maiduguri ba ta samun cikakken wutar lantarki.
“Mun sami damar daukar wutar lantarki ta wani tsohon layin da ya kai KV 33 wanda muka gyara tare da gyarawa sannan muka iya daukar megawatt 10 zuwa Maiduguri sama da kilomita 130 a kan wata hanya guda 33. Mun dawo da wancan wajen wata uku zuwa hudu ko wajen.