Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da ake yi cewa mahara na tserewa zuwa jiharsa ne bayan sun kai hari a jihar Benue.
Da jihar Nasarawa da jihar Benue maƙwabtan juna ne, wanda hakan ya sa wasu ke zargin maharan da suke addabar yankunan jihar Benue suna guduwa zuwa Nasarawa ne suna ɓoyewa har tashin hankalin ya lafa, sannan su koma su sake wani harin.
Daga cikin kashe-kashen jihar da aka yi irin wannan zargin, akwai kisan da aka yi a garin Yelwata na Benue na kwanakin baya, wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane da dama.
Sai dai a tattaunawarsa da tashar Channels a shirin Politics Today a daren Alhamis, Gwamna Sule ya musanta zargin, inda ya ce babu wannan maganar.
“Jihar Nasarawa na da nata matsalolin, me zai sa mu zama maɓoyar wasu mahara?” mu kanmu ta matsalolinmu na cikin gida muke, ba ɗauko matsalolin wasu ba. A Nasarawa ma ba mu da makiyaya da yawa.”
Sai dai ya ce tun lokacin da ya ƙarbi ragamar mulki a shekarar 2019 ya samu zargin, “har ta kai wanda na gada da gwamnan Benue na wancan lokacin, Ortom sun samu saɓani ba sa ma magana da wanda na gada. Da na shiga ofis, sai na kira Ortom muka zauna, ya kawo min ƙorafin, na ce masa za mu yi aiki tare domin magance ta.”