fidelitybank

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Date:

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da ake yi cewa mahara na tserewa zuwa jiharsa ne bayan sun kai hari a jihar Benue.

Da jihar Nasarawa da jihar Benue maƙwabtan juna ne, wanda hakan ya sa wasu ke zargin maharan da suke addabar yankunan jihar Benue suna guduwa zuwa Nasarawa ne suna ɓoyewa har tashin hankalin ya lafa, sannan su koma su sake wani harin.

Daga cikin kashe-kashen jihar da aka yi irin wannan zargin, akwai kisan da aka yi a garin Yelwata na Benue na kwanakin baya, wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane da dama.

Sai dai a tattaunawarsa da tashar Channels a shirin Politics Today a daren Alhamis, Gwamna Sule ya musanta zargin, inda ya ce babu wannan maganar.

“Jihar Nasarawa na da nata matsalolin, me zai sa mu zama maɓoyar wasu mahara?” mu kanmu ta matsalolinmu na cikin gida muke, ba ɗauko matsalolin wasu ba. A Nasarawa ma ba mu da makiyaya da yawa.”

Sai dai ya ce tun lokacin da ya ƙarbi ragamar mulki a shekarar 2019 ya samu zargin, “har ta kai wanda na gada da gwamnan Benue na wancan lokacin, Ortom sun samu saɓani ba sa ma magana da wanda na gada. Da na shiga ofis, sai na kira Ortom muka zauna, ya kawo min ƙorafin, na ce masa za mu yi aiki tare domin magance ta.”

tribune news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp