fidelitybank

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Date:

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da ake yi cewa mahara na tserewa zuwa jiharsa ne bayan sun kai hari a jihar Benue.

Da jihar Nasarawa da jihar Benue maƙwabtan juna ne, wanda hakan ya sa wasu ke zargin maharan da suke addabar yankunan jihar Benue suna guduwa zuwa Nasarawa ne suna ɓoyewa har tashin hankalin ya lafa, sannan su koma su sake wani harin.

Daga cikin kashe-kashen jihar da aka yi irin wannan zargin, akwai kisan da aka yi a garin Yelwata na Benue na kwanakin baya, wanda ya yi sanadiyar mutuwar mutane da dama.

Sai dai a tattaunawarsa da tashar Channels a shirin Politics Today a daren Alhamis, Gwamna Sule ya musanta zargin, inda ya ce babu wannan maganar.

“Jihar Nasarawa na da nata matsalolin, me zai sa mu zama maɓoyar wasu mahara?” mu kanmu ta matsalolinmu na cikin gida muke, ba ɗauko matsalolin wasu ba. A Nasarawa ma ba mu da makiyaya da yawa.”

Sai dai ya ce tun lokacin da ya ƙarbi ragamar mulki a shekarar 2019 ya samu zargin, “har ta kai wanda na gada da gwamnan Benue na wancan lokacin, Ortom sun samu saɓani ba sa ma magana da wanda na gada. Da na shiga ofis, sai na kira Ortom muka zauna, ya kawo min ƙorafin, na ce masa za mu yi aiki tare domin magance ta.”

the sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...

Sojoji sun mayar da martani kan ‘Yan ta’addan Neja

Dakarun Sojin Saman kasar nan, sun ce sun ƙaddamar...

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...

PDP ta yi watsi da matakin shugaban jam’iyyar da ya dauka

Kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP, ya yi watsi da...

Tinubu zai sanya hannu kan sabbin dokokin haraji

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai sanya hannu kan...

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...

Majalisar dokoki na son Iran ta yanke hulɗa da hukumar sanya ido kan makamashin nukiliya

Majalisar dokokin Iran ta kaɗa ƙuri’a domin yanke hulɗa...
X whatsapp