fidelitybank

‘Yan ta’adda 6 sun mutu yayin arangamar ISWAP da Boko Haram

Date:

Rahotanni sun bayyana cewa mayakan kungiyar ta’addanci ta Da’ish a yammacin Afrika (ISWAP), sun kai farmaki a yankunan bangaren Abubakar Shekau na kungiyar Boko Haram, inda suka kashe ‘yan ta’adda shida.

A cewar Zagazola Makama, kwararre kan yaki da tada kayar baya kuma mai sharhi kan harkokin tsaro a yankin tafkin Chadi, maharan sun kuma kwato bindigogin AK-47 guda biyar daga hannun ‘yan ta’addan na Boko Haram.

Majiyoyi sun ce lamarin wanda ya faru a karshen mako, da alama ci gaba ne a ci gaba da fafatawa tsakanin su da ‘yan ta’addan ISWAP a wani samame da suka kai gidan mayakan Boko Haram a Gajibo, wani gari mai tazarar kilomita 95 daga arewa maso gabashin Maiduguri, Borno. Babban birnin jihar, kuma sun kashe shida wadanda suka ayyana a matsayin “kafirai”.

Makama a shafinsa na yanar gizo ya rubuta cewa, “ISWAP ta sha kai hare-hare da dama a kan ‘yan ta’addan Boko Haram a ci gaba da rigimar da suke yi, wanda ya janyo hasarar kungiyar da asarar dukiyoyin yaki.

“Yarwar fadace-fadace tsakanin kungiyoyin masu jihadi, na iya kai su ga halakar da ba za a iya jurewa ba, kamar yadda kungiyar ISWAP mai tayar da kayar baya ta sha alwashin yin fafatawa da mambobin tsohuwar kungiyarta fiye da ma sojojin Najeriya”.

nigeria.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sudan ta Kudu ta yi ta’aziyyar Buhari

Mukaddashin Ministan Harkokin Wajen Sudan ta Kudu, Ambasada Akuei...

Trump ya na fama da cuta mai kumbura kafa da toshewar hanyar jini

A ranar Alhamis ne Fadar White House ta sanar...

Yadda aka gudanar da addu’o’in Buhari a Villa

A ranar Alhamis ne aka gudanar da addu'o'i ga...

Rasha tarnaki ce a wajen Tarayyar Turai – Jamus

Shugaban gwamnatin Jamus Friedrich Merz ya shaidawa BBC cewa...

Amurka ba ta goyon bayan Isra’ila a harin Syria – Trump

Amurka ta ce ba ta goyon bayan hare-haren da...

Tinubu zai zo Kano ta’aziyyar Dantata

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu zai kai ziyara Kano yau...

Tarayyar Turai tamince da ƙaƙaba wa Rasha sabbin takunkumai

Ƙungiyar Tarayyar Turai ta amince da ƙaƙaba wa Rasha...

Gwamnan Filato ya zargi Jami’ai da kin kama ‘yan bindiga

Gwamnatin jihar Filato ta zargi jami'an sojojin ƙasar da...

Za a yi wa Buhari addu’a a Abuja

Gwamnatin Tarayya za ta jagoranci gudanar da taron addu'o'i...

Buhari ya ban umarni na kula da Talakawan Najeriya – Peter Obi

Jagorar jam'iyyar LP a Najeriya, Peter Obi ya ce,...

Sojojin hadin gwiwa sun hallaka ‘yan Boko Haram a tafkin Chadi

Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a...

Na yi rashin aboki na gari kuma Najeriya ta rasa mutumin kirki – Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, na ci gaba da alhinin...
X whatsapp